spon

Showing posts with label duniya. Show all posts
Showing posts with label duniya. Show all posts

Thursday, December 28, 2017

Karanta yadda ake 'cin zarafin matan Nigeria a Facebook'


Shugaban Facebook, Marck Zukerberg ya ziyarci fadar shugaban da ya ziyarci Najeriya kwanakin baya
Wani bincike ya nuna cewa mata da dama a arewacin Najeriya su na kaurace wa intanet sakamakon barazana da cin zarafin da suke fuskanta daga ma'abota shafukan sada zumunta, musamman ma Facebook.
Kungiyoyin da ke fafutikar kare hakkin jinsi na kallon lamarin a matsayin wani nau'i na tauye 'yancin mata, wanda ke bukatar mahukunta su dauki matakan yaki da shi.
Wannan lamari ne ya sa Cibiyar Sasahar Sadarwa da ci gaban al'umma da ke Kano ta shirya wani taro don nazarin rahoton tare da duba hanyoyin magance matsalar.

Kungiyoyin da ke fafutikar kare hakkin jinsi na kallon lamarin a matsayin wani nau'i na tauye 'yancin mata
Ibrahim Isa ya tattauna da Mallam Muhammad Awwal Garba daga hukumar Hisbah ta jihar Kano da Maryam Ado Haruna, jami'a a wannan cibiya ta fasahar sadarwa da aka fi sani da CITAD, inda suka yi masa bayanin yadda girman matsalar take.
Ku latsa alamar lasifikar da ke kasa domin sauraron cikakkiyar hirar tasu:


Karanta yadda ake 'cin zarafin matan Nigeria a Facebook'


Shugaban Facebook, Marck Zukerberg ya ziyarci fadar shugaban da ya ziyarci Najeriya kwanakin baya
Wani bincike ya nuna cewa mata da dama a arewacin Najeriya su na kaurace wa intanet sakamakon barazana da cin zarafin da suke fuskanta daga ma'abota shafukan sada zumunta, musamman ma Facebook.
Kungiyoyin da ke fafutikar kare hakkin jinsi na kallon lamarin a matsayin wani nau'i na tauye 'yancin mata, wanda ke bukatar mahukunta su dauki matakan yaki da shi.
Wannan lamari ne ya sa Cibiyar Sasahar Sadarwa da ci gaban al'umma da ke Kano ta shirya wani taro don nazarin rahoton tare da duba hanyoyin magance matsalar.

Kungiyoyin da ke fafutikar kare hakkin jinsi na kallon lamarin a matsayin wani nau'i na tauye 'yancin mata
Ibrahim Isa ya tattauna da Mallam Muhammad Awwal Garba daga hukumar Hisbah ta jihar Kano da Maryam Ado Haruna, jami'a a wannan cibiya ta fasahar sadarwa da aka fi sani da CITAD, inda suka yi masa bayanin yadda girman matsalar take.
Ku latsa alamar lasifikar da ke kasa domin sauraron cikakkiyar hirar tasu:


Tuesday, December 26, 2017

Ana zaben shugaban kasa zagaye na biyu a Liberia

Ofishin hukumar zabe ta Liberiya a birnin Monrovia
A ranar Talata ne ne ake zaben shugaban kasa a Laberiya zagaye na biyu.
'Yan takara biyu ne dai za su fafata a zaben wanda shi ne karon farko da kasar ke shirya zabe don mika mulki daga wata sabuwar gwamnati zuwa wata tun bayan yakin basasar kasar.
Mataimakin shugaban kasar mai ci Joseph Boakai da kuma shahararren tsohon dan wasan kwallon kafan nan George Weah sune ke fafata wa.



Wasu dai na ganin hukumar zaben Laberiya ta yi gaggawar sake shirya zaben zagaye na biyu kafin shekarar ta kare.
Sai dai a hira da BBC, tsohon shugaban Nigeria Goodluck Jonathan, ya ce hukumar zaben ba ta yi gaggawar shirye zaben ba.
Mr Jonathan wanda ke jagorantar tawagar masu sa ido daga cibiyar bunkasa dimokradiyya ta National Democratic Institute, ya ce Laberiya tana da kalubale da dama na yadda shugaban kasa mai ci za ta mika mulki ga zababben shugaba.
Ya kara da cewa hakan zai nuna wa duniya cewa mulkin dimokradiya ya kafu sosai a Laberiya, kuma abun da ya rage shi ne a bunkasa tattalin arzikin kasar

Ana zaben shugaban kasa zagaye na biyu a Liberia

Ofishin hukumar zabe ta Liberiya a birnin Monrovia
A ranar Talata ne ne ake zaben shugaban kasa a Laberiya zagaye na biyu.
'Yan takara biyu ne dai za su fafata a zaben wanda shi ne karon farko da kasar ke shirya zabe don mika mulki daga wata sabuwar gwamnati zuwa wata tun bayan yakin basasar kasar.
Mataimakin shugaban kasar mai ci Joseph Boakai da kuma shahararren tsohon dan wasan kwallon kafan nan George Weah sune ke fafata wa.



Wasu dai na ganin hukumar zaben Laberiya ta yi gaggawar sake shirya zaben zagaye na biyu kafin shekarar ta kare.
Sai dai a hira da BBC, tsohon shugaban Nigeria Goodluck Jonathan, ya ce hukumar zaben ba ta yi gaggawar shirye zaben ba.
Mr Jonathan wanda ke jagorantar tawagar masu sa ido daga cibiyar bunkasa dimokradiyya ta National Democratic Institute, ya ce Laberiya tana da kalubale da dama na yadda shugaban kasa mai ci za ta mika mulki ga zababben shugaba.
Ya kara da cewa hakan zai nuna wa duniya cewa mulkin dimokradiya ya kafu sosai a Laberiya, kuma abun da ya rage shi ne a bunkasa tattalin arzikin kasar