spon

Showing posts with label labaran duniya. Show all posts
Showing posts with label labaran duniya. Show all posts

Monday, November 26, 2018

Sojojin sama sun tarwatsa wasu rundunonin Boko haram,bayen harin da aka kaiwa sojojin Nigeria a metele

Rundunar sojojin sama suntashi rundunar Boko haram bayan harin da akakaiwa rundunar sojojin Nigeria a (Metela) a barno
*adadin sojojin da akakashe yakai misalin 130 hakan neyasa yarazana rundunar sojojin kasar Nigeria
*Wannan harin yabigi kowa tundaga kan gwamnatin harzuwa al,umar kasannan

Thursday, November 1, 2018

ZAZZAFA:WAKAR GWANNA BARAWO MAI WAKA BARAWO

*wakar da akafitar zazzafa ta gwamna barawo mai waka barawo

GANDUJE VS JAFAR JAFAR

Thursday, October 18, 2018

TABBAS DAUKE WUTAR LANTARKI YANA GAB DA ZAMA TARIHI A KASARNAN

Kamar yadda boko Haram take dab da zama tarihi a Kasarnan....

Haka kuma rashin tsaro sai dai mu ba na bayanmu labarin cewar a baya anyi rashin tsaro....

Haka kuma fita waje don sawo kaya na tabbatar diyana da zan haifa nan gaba in sha Allah ba zasu fita waje don sawo kaya ba domin muna dab da kera komai made in Nigeria da yardar Allah.....

Haka kuma cin hanci a Kasarnan yana dab da zama tarihi......

Uwa Uba kuma Rashin aikinyi in Allah ya yarda nan gaba sai Kowa ya zabi irin aikin da yake son yi.......

Da yardar Allah sai Nigeria ta shiga cikin kasashe  mafi daraja a doron kasa..

Ya Allah ka taimaki Baba Buhari akan aniyarsa ta gyaran kasa

Wednesday, October 17, 2018

HABAICIN ATIKU GA BUHARI: ‘Ni ba zan shafe wata shida ban nada ministoci ba

                                      ATIKU VS BUHARI

Ali Artwork Yayi Raddi Ka Jaruman Da Suke Kare Ganduje

Shahararren Dan Comedy nan  kuma mai editing  na bidiyo na kannywood Ali Muhammad Idris wanda akafi sani da (Ali Artwork) ya kasance kwararen mai editi wanda kusan duk shekara shine yake zama gwarzon Shekara a bangaren masu editing, wanda kusan ya samu lambar yabo wato (Award) daga kungiyoyi da kamfanoni da dama.

Ya samu lambar yabo a wajan ministan gada labarai Lai Muhammad shine ya Bashi Kyautar warzon Ahekara A 2016,  ‘yan kwanakinnan ma anyi bikin karramashi tare da bashi lambar yabo a lagos.

Jarumin ya kware a fanin editing na bidiyo yana iya maida hoto mara motsi ya kuma yana motsi.

Dan haka jarumk Ali Artwork ya dabbatar da bidiyon Da Jafar Jafar ya saki na gwamnan kano wanda akace hawa akai, ali artwork yace bidiyon na gaske ne ba wai hadi.
Kuma yayi kira ga jaruman fim wadanda suke kokarin kare gwamna ganduje da su daina wahalar da kansu.

Dadin dadawa jarumin ya kara da cewa wai ba dan shi ya kasance magoyin bayan tsohon gwamna kwankwaso bane yace haka,

Kudai kalli bidiyon kuje cikake labarin daga bakinsa

Tuesday, October 16, 2018

Saudiyya na fusantar matsin lamba kan batan Jamal Khashoggi

Mr Pompeo ya gode wa Sarki Salman saboda jajircewa kan binciken
Ana kara matsa wa Saudiyya lamba kan ta yi cikakken bayani kan makomar dan jaridar nan Jamal Khashoggi, a daidai lokacin da sakataren harkokin wajen Amurka Mike Pompeo ya ke gana wa da sarki Salman a birnin Riyadh.
An yi wa Khasoggi ganin karshe a ofishin jakadancin Saudiyya da ke birnin Santabul na Turkiya mako biyu da suka gabata.
Hukumomin Turkiya na da yakinin cewa jami'an Saudiyya ne suka kashe dan jaridar, sai dai hukumomin Saudiyya sun musanta zargin.
Sai dai kafofofin watsa labaran Amurka na cewa, da alama Saudiyya na shirin tabbatar da cewa Khashoggi ya mutu a lokacin da aka samu matsala yayin da ake yi masa tambayoyi.
A dare daya, rundunar 'yan sandan Turkiyya ta gama binciken ofishin jakadancin bayan da hukumomin Saudiyya su ka ba su damar shiga.

Me zai fito daga tattaunawar Sarki Salman da Pompeo?

Sakataren harkokin wajen da sarkin sun gana a Riyadh.
Yayin da ba a bayyana abubuwan da suka tattauna ba, ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta ce Mista Pompeo ya yi amfani da damar wajen mika godiyarsa ga Sarki Salman kan "jajircewarsa, da binciken gaskiya" a kan bacewar Mr Khashoggi.
Ana kuma sa rai Mr Pompeo zai nemi karin bayani kan wata hira tsakanin sarkin da Shugaba Donald Trump ranar Litinin.
Mr Trump ya wallafa wani sako a shafinsa na Twitter cewa: "Yanzu na gama magana da Sarkin Saudiyya, wanda ya ce ba shi da masaniya kan abin da ya faru ga dan kasarsa."
Daga baya kuma, Trump ya shaida wa 'yan jarida cewar: "Ya musanta da kakkausar murya. A ganina, watakila 'yan bindiga ne suka kashe shi. Wa ya sani?"
Akwai abubuwa da dama tattare da wannan lamarin, ganin cewa akwai dangantaka mai karfi tsakanin Saudiyya da Amurka.
Mr. Trump dai ya riga ya bayyana cewa ba zai soke wata yarjejeniyar makamai mai tsoka ba tsakanin kasarsa da Saudiyya.
Amma ya yi barazanar yin hukunci mai tsauri idan aka gano masarautar da hannu a kashe Khashogi.
Sarki Salman ya bayar da umarnin yin bincike kan batan dan jaridar ranar Litinin.
Sai dai a jerin sanarwar da Saudiya ta fitar kawo yanzu, sun yi watsi da zargin da ake yi wa kasar kan kisan.
A na sa rai Mr Pompeo zai gana da yarima mai jiran gado Mohammed bin Salman a Riyadh.
Daga nan kuma sakataren harkokin wajen zai je Turkiyya.
Presentational grey line

Me ya faru a binciken ofishin jakadancin?

A karon farko tun bacewar dan jaridar ran 2 ga watan Oktoba, an kyale masu bincike a Turkiyya su shiga cikin ginin.
'Yan sandan Turkiyya sun yi bincike a ofishin jakadancin Saudiyya a SantambulHakkin mallakar hotoEPA
Image caption'Yan sandan Turkiyya sun yi bincike a ofishin jakadancin Saudiyya a Santambul
Tawagar Saudiyya ce ta fara shiga ranar Litinin, sai tawagar 'yan sandan binciken Turkiyya ta shiga.
An ruwaito cewar sun dauki samfurin kasar lambun ofishin jakadancin.

Abun da ake zargin ya faru a Satambul

Hotunan kyamarorin tsaro na CCTV sun nuna dan jaridar dan kasar Saudiyya yana shiga karamin ofihin jakadancin Saudiyya a birnin Santanbul na Turkiyya.
Gani na karshe da aka yi wa Mr Khashoggi, mai sukar gwamnatin Saudiyya a rubuce-rubucensa, ranar 2 ga watan Oktoba ne yayin da yake shiga ofishin jakadancin.
Rahotanni sun nuna cewa an far wa Khashoggi a ofishin bayan da ya shiga ya karbo takardun aurensa.
Majiyoyi a Turkiyya na ganin cewa wata tawagar karfafan mutane 15 masu kisa 'yan Saudiyya ce ta kashe shi, amma Saudiyyar ta dage a kan cewar ya fita daga ofishin cikin koshin lafiya.
A baya dai, Mr Khashoggi mai bai wa masarautar Saudiyya shawara ne kafin dangantakarsu ta yi tsami, inda daga baya ya yi gudun hijira na rajin kai.

Monday, October 15, 2018

Dadumi Duminta:Ashiryanake dana bawa Nigeria rance

Mainai man takara kujerar shugaban kasa wato Atiku Abubakar yace"Ashirya take dayabawa yen Nigeria rance

*Inda nazama shugaban kasa ashirye nake dabiyan ma,aikata akan lokaci,da kuma kara daukan ma,aikata
*yakara da cewa"Ashirya nake damabawa duk wani Dan Nigeria Wanda baya aikin gwamnati Albashin #20,000
*yakara da cewa"Ina da kudi shedane saidai nabawa yen Nigeria rance badai subani ba, za muyine kawai don farfado da arzikin kasar mu
*

Sunday, October 14, 2018

Kisan kai: 'Yan sanda na neman Salisu Sagir Takai


Rundunar 'yan sanda a jihar Kano da ke arewacin Najeriya na neman Salihu Sagir Takai dan takarar mukamin gwamna a karkashin jam'iyyar PDP da ya kai kansa ofishinsu ranar Litinin 15 ga watan Oktoba domin kare kansa daga zargin kisan wani dattijo mai shekara 70.
Sanarwar da kakakin rundunar, Sufritenda Magaji Musa Majiya ya sanyawa hannu a madadin
kwamishinan 'yan sandan jihar Rabi'u Yusuf.
Sanarwar 'yan sanda ta ce a ranar Asabar 13 ga watan Oktoba dan takarar gwamnan ya fito daga filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano akan hanyarsa ta zuwa gidansa tare da wasu magoya bayansa.
Magoya bayan da ke cikin tawagarsa sun sari wani dattijo mai shekara 70 da haihuwa a ka a daidai shataletalen Ahmadu Bello Way, lamarin da yayi sanadin mutuwarsa.
Sanarwar da 'yan sanda ta kuma ce magoya bayan Salihu Sagir Takai sun rika barnata dukkan allunan talla na 'yan takara masu adawa da shi a kan hanyarsu ta zuwa gidan nasa.
Sun kuma rika cin mutuncin al'ummar da suka hadu ta ita.
Sanarwar ta ce da wadannan dalilan ya zama wajibi ta kira dan takarar da ya bayyana mata dalilin da magoya bayansa suka dauki wadannan matakan na kisan kai da tayar da hankalin al'umma da barnata dukiyarsu.

Amma a nasa bangaren, Salihu Sagir Takai ya musanta cewa rundunar 'yan sanda jihar ta Kano sun gayyace shi zuwa ofishinsu akan wannan batu.
A wata hira da suka yi da Yusuf Ibrahim Yakasai na BBC, ya ce a shirye yake yaje wurinsu domin kare kansa daga wannan zargin.
Ya kuma musanta cewa magoya bayansa ne suka aikata dukkan laifukan da ake tuhumarsu da aikatawa.
Ya kuma yi Alla wadai da wannan abin da ya faru, inda yayi kira da hukumomi su gudanar da cikakken bincike a kan al'amarin domin gano wadanda ke da alhakin wannan aiak-aikar.
http://www.kannyonline.ga/2018/10/kisan-kai-yan-sanda-na-neman-salisu.htmlRead More

Saturday, September 29, 2018

RAHAMA SADAU TASAKE SAMU LAMBAR YABO

Har yanzu tauraron fitacciyar jaruma Rahama Sadau na cigaba da haskawa inda ya samu wani sabon lambar yabo a karshen makon da ya shude.


Jarumar ta samu kyautar jaruma mai bada taimako wajen haddasa zaman lafiya  a bikin Peace Achievers Awards 2018 wanda aka gudanar ranar Asabar 22 ga watan Satumba a dakin taro na Transcorp hilton Hotel dake Abuja.
Rahama ta nuna farin cikin ta samun wannnan kyautar a shafin ta na kafafen sada zumunta.

Gasar Peace Achievers Awards biki ne wanda aka gudanar a ko wani shekara domin karrama fitattun hukumomi da yan kasar dake taka rawar gani wajen raya zaman lafiya a kasar.

Bikin gasar na bana shine karo na bakwai.
Kyautar da jarumar ta samu shine na uku da zata samu bana bayan na jaridar Leadership da gidauniyar Global Women Empowerment network

Wednesday, September 12, 2018

ANTATTAUNA DA ISA MAJIYA SHUGABAN YANSANDA NAJAHAR KANO


  • Antattauna da Shugaban yansanda Najihar kano Game da Zarginda akewa Wata Jami,ar lpy

Bayan zuwan Bahari China yaba kodar yin Jirginsama

Bayan zuwan Genaral Buhari China ya bada kodar yin jirginsama

OH:Dantakarar Gwamna yabige da rawar gangi A jihar kano

Dan takarar Gwamna yabige da rawar Gangi a jihar kano

  • wani dan takara yafito campain yabige darawa tare da yen daba

Tuesday, September 11, 2018

2019 : Atiku Da Lamido Sun Shiga Tattaunawar Sirri

2019 : Atiku Da Lamido Sun Shiga Tattaunawar Sirri

Monday, September 10, 2018

'yen bindiga sunkai hari kan babban kamfainin man fetur a Libya


Smoke rises form the headquarters of Libyan state oil firm National Oil Corporation (NOC) on 10 September 2018
Image captionHayakin da ke fitowa daga kamfanin man ya turnuke yankin

Wasu 'yan bindiga sun kai hari kan hedikwatar babban kamfanin man fetur da ke Tripoli, babban birnin kasar Libya.
Jami'an tsaro mun yi taho-mu-gama da maharan a kamfanin da ke tsakiyar birnin, kuma ganau sun ce sun yi ta jin karar harbe-harben bindigogi da kuma fashewar abubuwa.
A makon jiya ne majalisar dinkin duniya ta bayar da sanarwar cewa kungiyoyin 'yan bindigar da ke fada da juna a babban binrin kasar su yi sulhu.
Gwamnatin da majalisar dinkin duniyar ke mara wa baya ce ke mulki a Tripoli.
Amma kungiyoyin masu tayar da kayar baya ne ke rike da akasarin kasar.
Wani ma'aikacin kamfanin man, wanda ya tsallake ta taga ya tsere daga ginin, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa uku daga cikin 'yan bindiga biyar sun yi ta harbi a cikin ginin inda suka samu mutane da dama.
Ganau sun gaya wa Reuters an fitar da shugaban kamfanin man, Mustafa Sanallah, daga ginin ba tare da samun ko da kwarzane ba.
Ma'aikatan ba da ceto sun isa wurin domin taimakawa mutanen da suka ji rauni.
Har yanzu babu tabbaci kan kungiyar da ta kai harin.



Abinda yasa nabar hakidar shi,a

  • Halima Abubakar KD

ABINDA YASA NABAR AQIDAR SHI'A.
Ni suna na Alhj Adam, mazauni kaduna, na kasance acikin wannan aqidar tun tuni har nakai matsayin shugaban HURRAS a yekinmu (ugw. Rimi) da kewaye. Wallahi wallahi wallahi wannan maganar dazan fada babu kage acikinta
Ni Alhamdulillah inada rufin asiri dai-dai gorgodo, sai nabiyawa kaina zuwa aikin haji.
An rege saura kwana kadan zamu tashi, abokaina wanda basai na kama suna ba, sukayimin rekiya zuwa airport, bayan zan tafi shiga jirgi sai suka cemin, zamu baka saqo idan kun sauka a madina, idan ka ziyarci Annabi SAW, ka la'anci wane da wane, sai bance musu komaiba nayi murmushi nashiga jirgi. Bayan mun sauka madina an kaimu masauki mukayi wanka nashirya sai natafi masallaci nayi nafila sai nazauna ina hutawa, take sai bacci ya daukeni, nan take sai nayi mafarki da Annabi SAW. Wallahi sai naga mutane biyu a tare dashi, damansa yace SAYYADI ABUBAKAR NE, hagunsa yacemin SAYYADI UMAR NE. Sai yace sune akabaka saqo kajefesu ka la'ancesu ko? To kafin kafara dasu kafara dani.
Wallahi sai nafara magiya ya Rasulullah kayi haquri wallahi ban amsamusuba, ni bazan iyaba hakanan dai sai yacemin kallican, dubawan dazanyi sai ga abokaina acikin irin wata wuta wacce bazan iya misaltataba, yacemin to can shine makoman mai zagin sahabbaina.
Nafarka daga bacci a firgice, sai nakira waya gida intambaya ina abokaina nayi ta kiran wayansu bata shiga......
Sai akacemin ai dasuka rakaka kafin sudawo sukayi hadari suka mutu, kuma dukkansu yan nan Kaduna ne.
Nadimauce sosai nan take nafita daga aqidar, nayi Allah wadai da ita.
Dan Allah idan kasamu wannan saqon katurama jama'a saboda katayani isarwa. Wallahi babu qage acikin wannan zancen, saboda qarya da Annabi SAW shine karshen bala'i.
Allah katsare mana imaninmu.

SHUGABA: SHUGABA MAI CI DA ADDINI MALAM IBRAHIM SHEKARAU YASAKE KALAMAN KARYA

MALAM IBRAHIM SHEKARAU YASAKE KALAMAN KARYA
Ga,abinda yake cewa"Manzon Allah ma da aka takura masa hijira yayi
Don haka nima da masoyana munyi hijira da ga PDP zuwa APC domin yaki da zalunci Akasa,cewar malam shekarau

Friday, September 7, 2018

Baba Buhari: Am back from china to figth corruption


Baba Buhari: Am back from china to figth corruption

AKIDUN ZAMANI: Shin ya dace mace ta yi aikin ofis?

AKIDUN ZAMANI: Shin ya dace mace tai aikin ofis.
 Author/arewainfinit
 Date/7 sep 2018
 
Akidun Zamani, tare da Fatima Zahra Umar, wani sabon fili ne inda za ku riƙa karanta ƙasida guda duk a mako kan batutuwan da suka shafi mata, masu daɗi da marasa daɗi. Manufar wannan filiita ce samar da wata dama don duba matsalolin da ke damun mata da kuma zaƙulo hanyoyin warware su. Sannan kuma za mu riƙa gabatar da tattaunawa a kan batutuwan da wannan fili ya taɓo a rediyo. Batun da ƙasidarmu ta yau ta yi nazari a kai shi ne "Matsayin mata masu fita aiki".
Mata masu aiki sun fi samun 'ya'ya masu ilimi, masu nutsuwa, kuma masu kokarin neman ci gaba. Na san haka batun yake, domin ni ma haka nake.
Akwai alfanun samun uwa ko mata mai yin aiki. Abin dubawa a nan shi ne idan wani abu ya samu maigidan (kamar mutuwa, rashin lafiya ko ya rasa aikin yi), ita matar ko uwar tana iya daukar nauyin gidanta, ba tare da ta zame wa kowa alaƙaƙai ba
Mutane da yawa suna ganin cewa mace bai kamata ta yi aiki ba, musammam ma idan tana da 'ya'ya. Masu wannan ra'ayin na ganin cewar matar da ke yin aiki na iya watsar da babban nauyin da ke kanta - na zama matar gida ko uwa, wanda abu ne da zai iya janyo mummunan tasiri ga gidanta.
Yawancin mutane na ganin cewa idan mace na yin aiki a wani wuri, yaranta ba za su samu kulawar ƙwarai ba. Mutane kuma na ganin cewa fitar da matar aure ke yi ka iya sanya wa idonta ya buɗe, wanda a ganinsu zai iya ɓata martabarta da ta 'ya'yanta.
Abin da ya kamata mu tambayi kanmu shi ne, shin aiki a wajen mace na iya ɓata tarbiyyar 'ya'ya, ko ya ɓata dangantakarta da mijinta?
Duk da yake, wasu daga cikin wadannan batutuwan haka suke, amma yawancin lamarin al'ada ce kawai. Wasu al'adun kan sa mu rasa ɗumbin alfanun samun mata a ma'aikatu.
A misali, ka ga ba mu da likitoci mata masu yawa a asibitocinmu. A matsayina na mace, ba ko yaushe nake son likita namiji ya duba ni ba, amma na san matan da suka kammala karatun likita, kuma suna gida zaune, ba sa yin aiki. Kawai don maigidan ba ya son ta rika cudanya da maza, amma kuma ya fi son likita mace ta duba matarsa idan ta je asibiti.
Dukkanmu mun san ƙissar Sayyida Khadija (RA) uwargidan Annabi Muhammad SAW. Sayyida Khadija babbar 'yar kasuwa ce, lokacin da ta auri Annabi SAW. Amma duk da yake ita ce uwargidansa ta fuskar kasuwanci (a matsayinsa na hadiminta a wajen kasuwancinta), ta kasance uwa kuma matar gida abar alfahari ga kowa.
Abin har ya kai ga shekaru bayan rasuwarta, Annabi Muhammad SAW yakan yi maganarta cike da martabawa, da soyayya. An ruwaito cewa sauran matansa sun rika kishinta saboda irin yabonta da yake yi.
Abin da nake son nunawa a nan shi ne babu wani dalilin da zai hana mace yin sana'a ko aiki, musammam mace mai nutsuwa da kamun kai.
Zuwa wajen aiki bai zama sanadin rasa mutuncinta ba, domin wannan ya shafi irin halin matar ne tun ainihi. Mata masu yawa sun samu nasarar hada aiki da rike gidansu ba tare da sun zubar da mutuncinsu ba... wannan manuniya ce cewa batun na alaƙa da karfin hali da jajircewa da kuma tarbiyya.
Babban ƙalubalen mata masu aiki ke fuskanta shi ne na tabbatar da ganin sun ba kowanne ɓangare haƙƙinsa.
Yaya za mu iya tabbatar da mun tafiyar da ayyukanmu, kuma mun ba 'ya'yanmu tarbiyya ta gari? Yaya za mu yi adalci tsakanin yin aiki ko sana'a da kula da gida?
Amsar mai sauki ce, muna bukatar mazajenmu su ƙara tallafa mana. Domin babu inda aka ce aikin kula da 'ya'ya da kuma ba su tarbiyya na mace ne ita kaɗai.
Ina kira ga maza magidanta da iyaye maza su ƙara taimaka wa mata wajen kula da gida da kuma 'ya'ya, su taimaka mana wajen sana'o'inmu kuma su yi alfahari da abubuwan ci gaba idan sun same mu.
Manzon Allah SAW ya yi, me zai hana kai ma ka yi?
Ga Fatima Zahra Umar da baƙin da ta gayyata don tattanawa a kan wannan batu

OH !DUNIYA ABIN TSORO WATA TSINTSUWA TAFA FADO TAZA TSOHUWA

wata tsuntsuwa tafado taxa ma tsohuwa a garin Abuja

Monday, September 3, 2018

RA'AYI: NA SAN DAI BA ZA A HANA ALLAH YI WA BUHARI HISABI BA

RA'AYI: NA SAN DAI BA ZA A HANA ALLAH YI WA BUHARI HISABI BA




RA'AYI:  Na San Dai Ba Za A Hana Allah Yi Wa Buhari Hisabi Ba

Daga Zee Taraba

Dan Allah masu yi wa Buhari makauniyar soyayya ida kun isa ku hana Allah ya yi masa hisabi ranar gobe tunda ku ba za ku fada masa gaskiya ba kuma ba za ku bari masu tsoron Allah su fada masa gaskiya ba.

Mun lura abun naku ya soma wuce gona da iri, har ta kai ga kuna zagin Malaman addini akan siyasar banza wadda kwata-kwata duk rantsi duk jimawa shekaru takwas kacal ake akan kujerar.

Mulkin Buhari babu hali Malami ya ce zai fito ya fadawa Buhari gaskiya sai a soma cewa wai malamin siyasa ne, idan kuma ya yaba Buhari sai a ce na addini ne tsabar son zuciya irin namu.

Wai shi Buhari yafi karfi a fada masa gaskiya ne?

A ce wai Malaman addini a ringa zagin su akan wani dan Siyasa wanda kullum shi a yabon kansa yake shi kadai tsabar son rai?

To bara ku ji na fada muku, idan kun hana a fada masa gaskiya a nan gidan duniya, to ku sani baku isa ku hana Allah ya yi masa hissabi ba bisa ga yadda ya gudanar da mulkinsa da kuma rayuwarsa ba ranar gobe.

Saboda haka a yi hattara dan Allah, Siyasa ba hauka bane.