spon

Showing posts with label labarai. Show all posts
Showing posts with label labarai. Show all posts

Monday, October 22, 2018

SAKO DAGA ABUBAKAR ABDUSSALAMU ZUWAGA YEN NIGERIA

Abubakar Abdussalam
Yace
*"Bantaba gani ganin mutum mai gskyba kamar shugaba muhammadu Buhariba"
"Dama nasan za,aruna tunda shugabannin yanzu sunbaci da zulunci dole mai girma Muhammadu buhari yasha wahala,
Amman indai yen Nigeria sukai hakuri za,adace

Monday, September 10, 2018

INADA YAKININ ZAN ZAMA PRESIDENT A 2019

INADA YAKININ ZAN ZAMA PRESIDENT A FADAR (BAKOLA SARAKI)

Friday, September 7, 2018

Baba Buhari: Am back from china to figth corruption


Baba Buhari: Am back from china to figth corruption

Mara hannu mai digirgir na son ya zama dan majalisa Mintuna 59 da suka wuc



Mara hannu mai digirgir na son ya zama dan majalisa

  • Mintuna 59 da suka wuce
Vitalis Lanshima ya rasa hannayensa ne a lokacin da yake yaro, amma wannan larurar ba ta hana shi neman ilimi ba.
Kuma ya samu tallafin zuwa karatu zuwa kasar Amurka a Jami'ar Ballarmine da ke kasar.
Bayan ya gama digiri na daya da na biyu, Vitalis wanda dan asalin jihar Filato ne yana kan hanyarsa na kammala nazarin samun digiri na uku.
Duk da cewa yana aiki a Amurka, Lanshima yana da burin zama dan majalisa mai wakiltar mazabar Jos ta Arewa da Bassa a majalisar wakilan Najeriya.

Sunday, September 2, 2018

Ba na tsoron fafatawa a zabe na gaskiya — Buhari

HOME/POST FILE UNDER LABARAI
AUTHOR:AREWAINFINIT
DATE:SUN SEP 2 2018
 
NIGERIA PRESIDENCY
Image captionGwamnan jihar Lagos, wanda ake rade-radin cewa zai fice daga APC, na cikin tawagar Shugaba Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce ba ya tsoron fafatawa a zabe idan za a gudanar da shi cikin gaskiya.
Shugaba Buhari ya bayyana haka ne a yayin ganawa da 'yan Najeriya mazauna kasar China a birnin Beijing inda yake ziyara.
A cewar sa, "Ba na jin tsoron karawa a zaben da za a gudanar cikin gaskiya saboda shi ne ya sa na zama shugaban kasa. Na san irin faman da na yi inda sau uku ina tsayawa takara ina faduwa zabe amma ina kalubalantar sakamakon sa a kotun koli."
"Da na fadi a zabe karo na uku na ce 'Allah ya saka min'; daga bisani aka yi amfani da fasahar na'ura wuririn gudanar da zabe kuma hakan ya taimaka mana,' in ji Shugaba Buhari.

(Wasu mutane 'ba sa so a daina zub da jini a Nigeria')

HOME/post file Under labarai/
Author /Arewainfinit/
Post Tittle:wasu mutane basa so a daina zubda jini a Nigeria.
Ministan tsaron Najeriya ya ce wasu kungiyoyin kasashen waje ba sa so a daina rikice-rikice a kasar.
Mansur Dan-Ali ya shaida wa cealkaluman da wasu kungiyoyin kasar waje ke fitar kan kashe-kashen da ake yi a Najeriya ba gaskiya ba ne.
Yana yin raddi ne game da rahoton da kungiyar da ke bincike a kan rikice-rikice ta International Crisis Group ta fitar kwanakin baya cewa rikicin manoma da makiyaya da ya faru a jihohin Benue, Filato, Adamawa, Nassarawa da kuma Taraba ya yi sanadin mutuwar akalla mutum 1300 tun daga watan Janairun 2018.
Kungiyar ta ce wadannan alkaluman sun nunka na mutanen da suka mutu sakamakon hare-haren kungiyar Boko Haram a wannan shekarar sau shida.Abin da mutane ba su gane ba shi ne [kungiyoyin nan] suna da tasu manufa, idan ka ga abubuwan da suke yi a Maiduguri, suna so su karfafa rikicin ya kara yawa ne, wadansu daga cikinsu ba sa son ya kare saboda a nan suke samun kudinsu," in ji ministan.
Sai dai babu wata shaida da BBC ta samu da ta gaskata wannan zargi.
Ministan ya kara da cewa bai san adadin sojojin kasar da aka kashe a rikice-rikicen da aka yi cikin wata uku ba.
Sai dai ya ce gwamnatinsu tana daukar matakai na shawo kan matsalolin tabarbarewar tsaro da ke faruwa a Najeriya.

Thursday, August 30, 2018

Yadda mata ke karuwanci don burge mutane a Kenya 30 Agusta 2018

Mata matasa na amfani da maza 'yan daduro wajen samun kudaden da za su yi rayuwa don burge mutane a kafafan sada zumunta a kasar Kenya.
Wata mai shirya fina-finai, Nyasha Kadandara, ta ce mata na amfani da karuwanci wajen kawar da talauci, amma kuma a yanzu ya zamo abin burgewa.
BBC ta gudanar da bincike a kan wasu mata uku.
Ta farko mai buge-buge ce, sunanta Kal, mace ce mai da amma kuma ba ta da miji kuma tana rawa a gidajen rawa musamman da daddare, sannan babban burinta shi ne ta zamo tauraruwa.
Ta je Kenya in da ta nemi mai kudin da zai dauki nauyinta wato daduron da zai cika mata burinta ta zama mawakiya.
Ta farko mai buge-buge ce, sunanta Kal, mace ce mai da amma kuma ba ta da miji kuma tana rawa a gidajen rawa musamman da daddare, sannan babban burinta shi ne ta zamo tauraruwa.

    Ta je Kenya in da ta nemi mai kudin da zai dauki nauyinta wato daduron da zai cika mata burinta ta zama mawakiya.

    Monday, July 9, 2018

    Jack Wilshere ya koma West Ham United

    Jack Wilshere ya buga wa Ingila wasa sau 34
    Tsohon dan wasan Arsenal Jack Wilshere ya koma West Ham kan yarjejeniyar shekara uku, inda ya ce ya koma kulob din da ya dade yana kauna tun yana yaro.
    Kwantiragin dan kwallon mai shekara 26 ta kare da Gunners a karshen watan Yuni.
    "Har yanzu ina tuna lokacin da nake goyon bayan West Ham a lokacin da ina karami, na sha kallonsu a filin wasa na Upton Park," a cewarsa.
    West Ham na kuma dab da kulla yarjejeniya domin sayen dan kwallon Ukraine Andriy Yarmolenko.
    An fahimci cewa kudin da aka amince da Borussia Dortmund ya kai fan miliyan £17.66.

    PDP ta yi kawance da jam'iyyu 40 'don doke Buhari'

    Babbar jam'iyyar adawa a Najeriya PDP ta kulla wani sabon kawance da wadansu jam'iyyu fiye da 40 da ke kasar, gabanin babban zaben shekarar 2019.
    Jam'iyyun sun sanar da hakan ne lokacin wani taro da suka yi a Abuja ranar Litinin, inda suka yi wa kawance lakabi da Coalition of United Political Parties (CUPP).
    Sanarwar ta biyo bayan sanya hannu kan wata yarjejeniya da suka cimma da shugabannin jam'iyyun,"don kayar da Shugaba Muhammadu Buhari a zaben 2019," a cewarsu
    Yarjejeniyar ta kunshi wani shiri ta yadda za su tsayar da dan takara daya tilo a zaben shugaban kasa, da na gwamnoni a jihohi da kuma kujerun majalisa.
    Sai dai zuwa yanzu jam'iyya mai mulki ta APC ba ta mayar da martani ba, game da batun.
    Cikin wadanda suka halarci taron har da shugaban sabuwar jam'iyyar APC Injiniya Buba Galadima da kuma mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Ike Ekweremadu da sauransu.
    A shekarar 2015 ne jam'iyyar APC ta doke PDP a babban zaben kasar, bayan ta shafe shekara 16 tana mulkin kasar.

    An Kai Sabbin Hare Hare Kan Fulani A Filato

    An Kai Sabbin Hare hare Kan Fulani A Filato
    __¥___
    *
    Rundunar ‘yan sandan jihar Filato ta tabbatar cewa wasu matasa ‘yan kabilar Birom sun kai wasu hare hare a kan wasu makiyaya Fulani da ke zaune kusa da kwalejin ‘yan sanda da ke garin Buruku a karamar hukumar Jos ta Yamma.




    Rahotanni sun nuna cewa, babu wanda ya rasa ransa a yayin harin sai da wasu Fulani su biyu da aka yi wa rauni da kuma wata karamar saniya da aka kashe. Kakakin Rundunar ‘Yan sanda, Tyopev Terna ya tabbatar da cewa an warware rikicin bayan wani zama da aka yi tsakanin masu ruwa da tsaki a rikicin.
    #Rariya

    Zaben Gwamnan Ekiti: Yadda Aka Bada Tsaro

    ZABEN GWAMNAN EKITI: A yayin da ake shirye shiryen zaben kujerar Gwamnan Ekiti a ranar Asabar mai zuwa, Shugaban ‘Yan sanda na Kasa, Ibrahim Idiris ya tura ‘yan sanda 30,000, karnuka na musamman, jiragen masu saukar Angulu guda biyu, kananan motocin yaki 10, motocin sintiri 250, sai mataimakinsa, da kwamishinonin ‘yan sanda hudu don tabbatar da tsaro.

    A yayin da Hukumar Kiyaye Hadurra ta Kasa ( FRSC) ta tura jami’anta har 500, motocin sintiri 24, motocin daukar marasa lafiya guda uku.

    RANAR WANKA...

    RANAR WANKA...

    Hakikanin Abin Da Ya Jawo Rikici Na Da Kwankwaso, Cewar Gwamna Ganduje

     “Kun taba jin muna fada a lokacin da yake (Kwankwaso) Gwamna? San-sam. Ina yi masa biyayya a matsayinsa na Gwamna kuma Ubangidana. Lokacin da Buhari ya fada mani cewa zai yi takarar Shugabancin Kasa, na fada masa cewa ni Kwankwaso zan zaba. Shugaban Kasa (Buhari) ya ji dadin yadda na bayyana masa gaskiyata ba kwane-kwane. Dukkanmu da muka je Legas sai muka zabi Kwankwaso kuma duk da cewa mun fadi zaben amma dai ba mu munafunce shi (Kwankwaso) ba. Ya kasance shugabanmu a Kano, duk da cewa talakawan Kano Buhari suka zaba, mu Kwankwaso muka zaba…
    *
    “Sai dai abin takaici, Kwankwaso ba ya kallona ko amincewa da ni a matsayin Gwamna, ya yi zaton ladabin da nake masa a matsayina na Mataimakinsa kamar ni wawa ne.
    *
    “Ka tambayi duk wanda ya san ni, ba na kaskantar da duk wani tsohon Gwamna. Dangantakata da Shekarau mai girma ce kuma mai kyau, shi ma yana daraja ni a matsayina na Gwamna. Shin mene ne yake haddasa rashin jituwa tsakanina da Kwankwaso? Matsalar ba daga gare ni ba ce ko daya, shi ne dai yake son amfani da al’ummar Kano da dukiyar Kano domin ya kalubalanci Shugaban Kasarmu da muke jam’iyya daya. Haba! Ba zan taba amincewa da haka ba, domin Buhari ya taimaka mana a lokacin da ma ba jam’iyya daya muke da shi ba. Buhari ba mamugunci ba ne, ba zai iya makirci don kaskantar da kowa, ko raba shi da mukaminsa ba. Shi ne Shugaba a yau. Da Kwankwaso ne ya ci zaben, ba zan bari Buhari ya wulakanta shi ba.
    *
    “Duk wanda ke son barin (APC), ya bari kawai. Mu yi siyasa mai tsafta, mai natsuwa…”

    Fassara: Bashir Yahuza Malumfashi

    DA DUMIDUMINSA

    DA DUMIDUMINSA

    Membobin Sabuwar Jam'iyyar APC Da Na PDP Sun Yi Zaman Kulla Yarjejeniya Domin Kada Buhari A Zaben 2019

    Majalisar Borno Ta Tsayar Da Shettima Takarar Sanata

    Majalisar Borno Ta Tsayar Da Shettima Takarar Sanata
    __¥___
    *
    'Yan majalisar dokokin jihar Borno sun nemi Gwamnan jihar, Kashim Shettima kan ya fito takarar kujerar dan majalisar Dattawa na Borno ta Tsakiya.

    Kakakin Majalisar, Abdulkarim Lawan ya ce, ya zama dole Gwamnan ya fito takara don al'ummar mazabarsa sun amfana da irin kwarewarsa da iliminsa. Tun da farko dai, Gwamnan Shetiima ya fito fili ya nuna cewa idan har wa'adinsa ya cika, zai koma aikin koyarwa ne.

    JIYA BA YAU BA

    JIYA BA YAU BA

    AREWA UWAR DADI: Wani ayarin mutane a kan kekuna suna tafiya a Zaria a shekarar 1960.

    A lokacin babu ciwon hawan jini.
    Allah ya kara mana lafiya.

    Madogara: Uwa Idris

    Sunday, July 8, 2018

    Yanzu An Gama Da Boko Baram, Saura Gyara Yankunan Da Suka Barnata, Inji Buhari


    Yanzu An Gama Da Boko Baram, Saura Gyara Yankunan Da Suka Barnata, Inji Buhari

    Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce yanzu yankin arewa maso gabas yana matakin daidaita lamurra bayan rikicin Boko Haram.

    Da ya ke jawabi ga sojojin Nijeriya a garin Munguno a ziyarar da ya kai jihar Borno a ranar Juma'ar da ta gabata, Buhari ya ce "ta tabbata cewa yanzu muna cikin mataki ne na kokarin daidaita lamurra bayan rikici Boko Haram, kuma hakan ya samu ne saboda kyakkyawan aikin sojojinmu".

    Shugaba Buhari ya kuma kara da cewa mayakan Boko Haram da kansu suke mika wuya, kamar yadda kamfanin dillacin labaran AFP ya ruwaito.

    Bayanin shugaban a Munguno kamar yana nufin an kawo karshen tashin hankalin da jihohin arewa maso gabashin Nijeriya suka yi fama da shi a kusan shekara tara.

    Rundunar sojin Nijeriya da gwamnatin Buhari sun dade suna ikirarin kawo karshen rikicin Boko Haram wanda ya yi sanadin salwantar dubban rayuka a arewacin Najeriya tare da raba miliyoyi da gidajensu.

    Tun a yakin neman zabensa, Buhari ya alwashin zai kawo karshen rikicin Boko Haram da ya shafi kasashen da suka kewaye tafkin Chadi, Nijar da Kamaru da Chadi.

    Sai dai kuma har yanzu Boko Haram na ci gaba da yin barazana a yankunan inda ko a watan da ya gabata an kashe mutane 43 a hare haren kunar bakin wake da aka kai a garin Damboa a jihar Borno.

    Kashe-kashen da ake samu a rikicin makiyaya da manoma da kuma harin 'yan fashi a wasu jihohin Nijeriya wani babban kalubale ne na tsaro ga Buhari wanda ya ayyana neman wa'adin shugabanci na biyu.

    PDP Ta Kalubalanci Buhari Kan Ya Kori Ministar Kudi Kan Shaidar Yiwa Kasa Hidima Ta Bogi

    PDP Ta Kalubalanci Buhari Kan Ya Kori Ministar Kudi Kan Shaidar Yiwa Kasa Hidima Ta Bogi
    __¥___
    *
    Jam'iyyar PDP ta kalubalanci Shugaba Muhammad Buhari kan ya gaggauta korar Ministar Kudi, Kemi Adeosun tare kuma d hukunta ta bisa amfani da shaidar kammala bautar kasa (NYSC) ta bogi.

    Sakataren Jam'iyyar na Kasa, Kola Ologbondiyan ya ce a halin yanzu ta tabbata cewa gwamnatin Buhari na cike da barayi, 'yan damfara da mutane marasa gaskiya inda ya jaddada cewa kada Buhari ya kuskura ya kyale Ministar wanda yin hakan zai nuna cewa ba da gaske yake yi ba game da shirin yaki da rashawa da ya kaddamar.

    Monday, June 25, 2018

    Ban Yi Nadamar Kasancewar Adilin Mutum Ba — Buhari

    Ban Yi Nadamar Kasancewar Adilin Mutum Ba — Buhari
    __¥___
    *
    Shugaba Muhammad Buhari ya yi ikirarin cewa bai taba yin nadamar kasancewar adilin mutum ba inda ya jaddada cewa yana farin cikin yadda ya hana ‘yan uwansa da makusantarsa daga amfana da wata kwangilar gwamnati.

    Shugaban ya yi wannan ikirarin ne a lokacin da al’ummar Urhobo suka ziyarce shi a fadarsa a karkashin jagorancin Sheikh Hadiyyatullahi Abdulrashid inda ya nuna cewa shi bai bada kwangila kuma bai damu ya san wanda aka kwangila ba muddin zai yi aiki mai kyau kuma a farashin da zai karbu ga al’ummar kasa.


    #Mikiya

    Tuesday, June 5, 2018

    Majalisun Nijeriya Sun Gindaya Wa Shugaba Buhari Wasu Dokoki Guda 12


    Majalisun Nijeriya Sun Gindaya Wa Shugaba Buhari Wasu Dokoki Guda 12

    ...idan bai bi ba za mu dauki mataki, cewar majalisun

    Majalisun dokokin Nijeriya sun amince da wasu kudurori 12 da suka ce wajibi ne gwamnatin Muhamadu Buhari ta aiwatar da su ko kuma su dauki mataki.

    Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Bukola Saraki ne ya karanta matsayar da suka cima bayan wani zama na musamman da suka yi domin duba halin da kasar take ciki, wanda wasunsu suka ce yana ci gaba da tabarbarewa.

    Ya ce majalisun biyu sun amince cewa wajibi ne Shugaba Buhari ya dauki alhakin abubuwan da mutanen da ya nada suke yi, sannan ya dauki mataki kan duk wanda ya saba wa doka da yin barazana ga demokuradiyya.

    Suka kara da cewa wajibi ne jami'an tsaro su tunkari kashe-kashen da ake yi a kasar, sannan a daina takura wadanda ake wa kallon 'yan adawa ne ko kuma masu bambancin ra'ayi da bangaren zartarwa.

    "Majalisa ba za ta yi wata-wata ba wurin daukar mataki kamar yadda tsarin mulki ya ba ta dama, idan aka ki yin wani abu domin aiwatar da wadannan kudurori da aka a mince da su yau (Talata)".

    Wannan zama na zuwa ne a lokacin da rashin jituwa ke kara fitowa fili tsakanin gwamnatin Muhammadu Buhari da kuma shugabannin majalisar.

    Kudurori 12

    *Kawo karshen kashe-kashe a NajeriyaA daina tsangwama da kuma muzguna wa wadansu 'yan majalisa

    *Gwamnati ta rika bin doka da oda

    *Shugaban kasa ya dauki mataki kan wadansu wadanda ya nada mukamai

    *Ya yi yaki da cin hanci da rashawa tsakaninsa da Allah

    *Ya daina sanya baki kan al'amurran da suka shafi majalisar

    *Majalisar dokokin kasar za ta fara tuntubar Majalisar Dinkin Duniya don ceto demokradiyyar Nijeriya

    *Majalisar za ta tuntubi kungiyoyi masu rajin kare demokradiyya don ceto demokradiyyar kasar

    *Shugaban kasa ya magance matsalar rashin aikin yi da kuma talauci a kasar

    *Duka majalisoshin biyu sun nuna goyon baya ga shugabancin Bukola Saraki da kuma Yakubu Dogara

    *Kuma ba sa goyon shugabancin Sufeto Janar na 'yan sandan Nnjeriya Ibrahim Idris

    *Majalisa za ta dauki mataki kamar yadda tsarin mulki ya ba ta dama, idan aka ki yin wani abu.

    Wadansu na ganin barazanar daukar matakin da tsarin mulki ya ba su kamar yadda suka yi ikirari zai iya hada wa da yunkurin tsige Shugaba Buhari

    A ranar Litinin 'yan sandan kasar suka gayyaci Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Bukola Saraki domin amsa tambayoyi kan zargin daukar nauyin 'yan fashi da makami a mahaifarsa ta jihar Kwara.

    Sai dai daga bisani Sanata Saraki ya ce sun shaida masa cewa sun janye gayyatar, kawai suna bukatar "ya amsa ne a rubuce".

    Tsoffin 'yan sabuwar PDP sun fasa ganawa da OsinbajoAPC ta sha kaye a hannun PDP a zaben jihar Oyo

    Rahotanni sun kuma ce an rage yawan jami'an tsaron farin kaya da ke bin tawagar Saraki da kuma Kakakin Majalisar Wakilai Yakubu Dogara, da kuma mataimakansu.

    Wannan batu ne kuma ya sa kungiyar tsoffin 'yan sabuwar PDP, wacce Saraki da Kakakin Majalisar Wakilai Yakubu Dogara ke kan gaba a ciki, suka ce sun dakatar da tattaunawar da suke yi da gwamnatin kasar da kuma jam'iyyar APC.

    Suna dai zargin cewa an mayar da su saniyar-ware ne tare da yi musu bi-ta-da-kulli, a gwamnatin da suka taimaka aka kafa.

    A baya dai gwamnatin ta sha musanta wannan zargi.

    " Dalilin Da Ya Sa Buhari Bai Rattaba Hannu Kan Kasafin Kudin Bana Ba"

    " Dalilin Da Ya Sa Buhari Bai Rattaba Hannu Kan Kasafin Kudin Bana Ba"
    ___¥___
    *
    Ministan Kasafin kudi da tsare tsaren kasa, Sanata Udoma Udo Udoma ya bayyana cewa a halin yanzu Shugaba Muhammad na nazari kan daftarin kasafin kudin 2018 wanda majalisar tarayya ta mika masa.

    Ministan ya ce, yin nazarin ya zama dole don zakulo wuraren da aka tafka Kurakurai da aringizo. Tun watan Nuwamba na shekarar 2017 ne, Buhari ya mikawa majalisar kasafin kudin wanda aka tsara kashe Naira Tiriliyqn 8.6.