spon

Wednesday, January 24, 2018

Me 'yan Nigeria ke cewa kan wasikar Obasanjo ga Buhari?


Muhawara ta barke tsakanin 'yan Najeeriya kan wasikar da Obasanjo ya rubutawa Buhari
Wasikar da tsohon shugaban kasar Najeriya Olusegun Obasanjo ya fitar a ranar Litinin inda yake bai wa Shugaba Buhari shawara cewa kar ya sake yin tazarce a 2019 ta jawo muhawara mai zafi a tsakanin 'yan kasar.
Muhawarar ta barke a shafukan sada zaumunta da ma kafafen watsa labarai daban-daban inda mutane ke ci gaba da tofa albarkacin bakinsu.
A cikin bwasikar wacce Obasanjo ya aikewa manema labarai, ya caccaki Shugaba Buhari da cewa kamata ya yi ya bar mulki a 2019 ya je ya huta saboda yawan shekaru da yanayin lafiyarsa.
Ya kuma fiddo da wasu abubuwa da ya kira nakasu da kasar ke fuskanta wadanda a dalilinsu ne a zaben 2015 mutane suka fita kwai da kwarkwata don zabar Buhari da yakinin cewa shi ne zai magance musu wadannan matsaloli, "amma sai ga shi ba ta sauya zani ba," in ji tsohon shugaban kasar.
A baya dai


A shafukan Twitter da Facebook dai mutane sun ta bayyana ra'ayoyinsu inda wasu ke ganin lallai maganganun Obasanjo gaskiya ne kuma a kan hanya suke.
JJ Omojuwa wani fitaccen mai amfani da shafin twitter ne ya kuma rubuta cewa: "Argh! Lallai wannan alama ce da ke nuna cewa 2019 ta sako kai. Obasanjo bai taba fadar magana irin wannan a kan shugaban kasa kafin zabe ba kuma ba ta faru ba. Ga 'yan kallo irin ku da dama, za ku iya cewa lallai wannan ce shimfida ta abun da zai faru a zaben 2019."
Wasu kuwa cewa suke lallai Mista Obasanjo bai taba faduwa wani zabe da shi ya tsaya takara ko ya marawa wani baya ba tun daga shekarar 1999 da 2003 da 2007 da 2011 da kuma 2015.
Da zabukan da ya tsaya karkashin PDP guda hudu, da wanda ya marawa APC baya guda daya, a yanzu kuma ga shi ya nuna alkiblarsa ba tare da marawa ko wacce jam'iyya baya ba. Ko me zai faru?
Ita ma Nedu Okeke wacce take shafin Twitter da sunan @Nedunaija got=yon bayan wasikar ta yi da cewa: "Obasanjon da ya mara maka baya a 2015 ma ya ba ka shawara da cewa kar ka sake tsayawa takara saboda gazawarka.
"Matarka da ta goyi bayanka a 2015 ma ta nuna alamar cewa ba za ta sake goyon bayanka ba. Baba, don Allah ka tafi gida
Kazalika a hannun guda kuma akwai dumbin mutanen da suke sukar Obasanjo kan wannan wasika da ya aike wa Buhari.
@abubakar471 ya rubuta cewa: "Idan har obasano zai tsayar mana da 'yan takara sau uku, kuma dukkansu ba shugabanni na-gari ba ne, to don me ya sa zan gaskata son ransa a yanzu?"
Wani kuwa mai suna Parodidant Buhari a Twitter ya rubuta cewa: "Ga dukkan alamu Obasanjo bai san cewa bai yi tsufa da shiga gidan yari ba."

Babbar jam'iyyar adawa ta PDP a nata martanin cewa ta yi: Tsohon shugaban Najeriya ya tabbatar da matsayin da muka dade a kansa cewa gwamnatin Buhari da APC sun gaza a ko wanne fanni.
"Sai dai muna kira ga mutane da kar su yarda da kirkiro wata sabuwar kungiyar siyasa kamar yadda ake ta kira, maimakon haka gara su marawa PDP baya don ta ceto su."
Shi kuwa shugaban jam'iyyar APGA Dr. Victor Oye, cewa ya yi "Dr. Obasanjo bai cancanci shawartar Buhari kar ya sake tsayawa takara ba, kuma ya daina jawo tayar da hakarkari ba gaira ba dalili."
Wannan dai ba shi ne karo na farko da Obasanjo ya taba aikewa wani shugaban kasa wasika cewa kar ya yi tazarce ba, a baya ma ya taba aikewa tsohon Shugaba Goodluck Jonathan wasika cewa kar ya yi ta-zarce a 2015.
Wannan batu dai zai ci gaba da jan hankalin 'yan Najeriya a ciki da wajen kasar, sai dai babu tabbas ko wannan kira na Obasanjo zai yi tasiri ko ba zai yi ba, musamman ganin cewa wannan shekara ta 2018 ita ce wacce za a bambance tsakanin aya da tsakuwa kafin zaben 2019.

Me 'yan Nigeria ke cewa kan wasikar Obasanjo ga Buhari?


Muhawara ta barke tsakanin 'yan Najeeriya kan wasikar da Obasanjo ya rubutawa Buhari
Wasikar da tsohon shugaban kasar Najeriya Olusegun Obasanjo ya fitar a ranar Litinin inda yake bai wa Shugaba Buhari shawara cewa kar ya sake yin tazarce a 2019 ta jawo muhawara mai zafi a tsakanin 'yan kasar.
Muhawarar ta barke a shafukan sada zaumunta da ma kafafen watsa labarai daban-daban inda mutane ke ci gaba da tofa albarkacin bakinsu.
A cikin bwasikar wacce Obasanjo ya aikewa manema labarai, ya caccaki Shugaba Buhari da cewa kamata ya yi ya bar mulki a 2019 ya je ya huta saboda yawan shekaru da yanayin lafiyarsa.
Ya kuma fiddo da wasu abubuwa da ya kira nakasu da kasar ke fuskanta wadanda a dalilinsu ne a zaben 2015 mutane suka fita kwai da kwarkwata don zabar Buhari da yakinin cewa shi ne zai magance musu wadannan matsaloli, "amma sai ga shi ba ta sauya zani ba," in ji tsohon shugaban kasar.
A baya dai


A shafukan Twitter da Facebook dai mutane sun ta bayyana ra'ayoyinsu inda wasu ke ganin lallai maganganun Obasanjo gaskiya ne kuma a kan hanya suke.
JJ Omojuwa wani fitaccen mai amfani da shafin twitter ne ya kuma rubuta cewa: "Argh! Lallai wannan alama ce da ke nuna cewa 2019 ta sako kai. Obasanjo bai taba fadar magana irin wannan a kan shugaban kasa kafin zabe ba kuma ba ta faru ba. Ga 'yan kallo irin ku da dama, za ku iya cewa lallai wannan ce shimfida ta abun da zai faru a zaben 2019."
Wasu kuwa cewa suke lallai Mista Obasanjo bai taba faduwa wani zabe da shi ya tsaya takara ko ya marawa wani baya ba tun daga shekarar 1999 da 2003 da 2007 da 2011 da kuma 2015.
Da zabukan da ya tsaya karkashin PDP guda hudu, da wanda ya marawa APC baya guda daya, a yanzu kuma ga shi ya nuna alkiblarsa ba tare da marawa ko wacce jam'iyya baya ba. Ko me zai faru?
Ita ma Nedu Okeke wacce take shafin Twitter da sunan @Nedunaija got=yon bayan wasikar ta yi da cewa: "Obasanjon da ya mara maka baya a 2015 ma ya ba ka shawara da cewa kar ka sake tsayawa takara saboda gazawarka.
"Matarka da ta goyi bayanka a 2015 ma ta nuna alamar cewa ba za ta sake goyon bayanka ba. Baba, don Allah ka tafi gida
Kazalika a hannun guda kuma akwai dumbin mutanen da suke sukar Obasanjo kan wannan wasika da ya aike wa Buhari.
@abubakar471 ya rubuta cewa: "Idan har obasano zai tsayar mana da 'yan takara sau uku, kuma dukkansu ba shugabanni na-gari ba ne, to don me ya sa zan gaskata son ransa a yanzu?"
Wani kuwa mai suna Parodidant Buhari a Twitter ya rubuta cewa: "Ga dukkan alamu Obasanjo bai san cewa bai yi tsufa da shiga gidan yari ba."

Babbar jam'iyyar adawa ta PDP a nata martanin cewa ta yi: Tsohon shugaban Najeriya ya tabbatar da matsayin da muka dade a kansa cewa gwamnatin Buhari da APC sun gaza a ko wanne fanni.
"Sai dai muna kira ga mutane da kar su yarda da kirkiro wata sabuwar kungiyar siyasa kamar yadda ake ta kira, maimakon haka gara su marawa PDP baya don ta ceto su."
Shi kuwa shugaban jam'iyyar APGA Dr. Victor Oye, cewa ya yi "Dr. Obasanjo bai cancanci shawartar Buhari kar ya sake tsayawa takara ba, kuma ya daina jawo tayar da hakarkari ba gaira ba dalili."
Wannan dai ba shi ne karo na farko da Obasanjo ya taba aikewa wani shugaban kasa wasika cewa kar ya yi tazarce ba, a baya ma ya taba aikewa tsohon Shugaba Goodluck Jonathan wasika cewa kar ya yi ta-zarce a 2015.
Wannan batu dai zai ci gaba da jan hankalin 'yan Najeriya a ciki da wajen kasar, sai dai babu tabbas ko wannan kira na Obasanjo zai yi tasiri ko ba zai yi ba, musamman ganin cewa wannan shekara ta 2018 ita ce wacce za a bambance tsakanin aya da tsakuwa kafin zaben 2019.

2019: 'Batun tazarce ba shi ne a gaban Buhari ba'


  1. Ministan ya ce hauhawar farashin kayayyaki ya ragu da kashi 15 cikin 100 a watanni 11 a jere

Ministan yada labaran Najeriya Lai Mohammed ya ce maganar sake tsayawa takara ba shi ne a gaban Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ba a wani martani da ya yi ga tsohon Shugaba Olusegun Obasanjo.
  1. Ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya aike wa BBC ranar Laraba.
    A ranar Talata ne Mista Obasanjo ya rubuta wata budaddiyar wasika wadda ya ba Shugaba Buhari shawara kan kada ya sake tsayawa takara a zaben shekarar 2019.
    Jami'in gwamnatin ya ce wajibi ne a yaba wa Buhari kan abubuwa biyu cikin ukun da aka yi kamfe a kansu; wato yaki da cin hanci da rashawa da kuma yaki da masu tada kayar-baya.
    Har ila yau, ministan ya ce tsohon shugaban ya ce gwamnatin Buhari ba ta samu nasara ba a fannin tattalin arziki saboda shi ne na uku cikin jerin alkawurran da aka yayin kamfe.
    Daga nan ya ce yana ganin cewa aikace-aikacen Obasanjo ne ba su "ba shi sukunin fahimtar dimbin ayyukan ci gaban da gwamnatin Buhari take gudanarwa ba a halin yanzu musamman a fannin bunkasa tattalin arziki."
    Ministan ya kuma ce dukkan alkalumman da ake amfani da su wajen bayyana karfin tattalin arziki sun nuna cewa Najeriya na samun ci gaba.
    Hakazalika ya ce kasar ta fita daga matsin tattalin arziki ne ta hanyar amfani da shawarwarin da wadansu 'yan kasar suke ba ta.
    Bugu da kari, ministan ya ce hauhawar farashin kayayyaki ya ragu da kashi 15 cikin 100 a watanni 11 a jere.
    Ya ce fito tsarin amfani da asusu na bai daya wato (TSA) ya sa gwamnatinsu ta tara naira biliyan 108 kuma ya ce kasar tana adana fiye da naira biliyan 24 a kowane wata daga sabon tsarin.
    Jami'in gwamnatin ya ce sun samu naira biliyan 120 bayan sallamar ma'aikatan bogi. Haka dai ministan ya yi ta zayyana nasarorin da gwamnatin ta samu daya bayan daya a cikin sanarwar.
  2. Kan batun rikicin manoma da makiyaya ya ce gwamnatinsu a shirye take ta kawo karshen matsalar duk da cewa gadon matasar suka yi daga gwamnatin da ta gabace su, kamar yadda ya ce.
    Daga nan ya bukaci 'yan kasar da su ba su goyon baya don ganin an magance hakan.
    Game da batun tazarcen shugaban kuwa, ministan ya ce da gaske na wadansu 'yan kasar suna kiraye-kirayen neman ya sake tsayawa takara, yayin da wadansu kuma suke nuna adawarsu ga hakan.
    "Muna ganin wannan batun zai iya raba hankalin shugaban a halin yanzu saboda ya dukufa a kowace sa'a don ganin ya magance dimbin matsalolin da suke ci-wa kasar tuwo a karya wadanda galibinsu gadonsu ya yi daga tsoffin gwamnatocin da suka gabata," in ji shi.
    Har ila yau ya ce ba su taba tunanin cewa tsohon Shugaba Obasanjo yana da wata manufa ba kan wasikar bayan ci gaban kasa.
    "Mun karbi shawarwarinsa da zuciya daya kuma muna gode masa kan yadda ya samu lokaci duk da dimbin aikace-aikacen da ke gabansa ya rubuta mana wannan doguwar wasikar," in ji ministan.
    Ita ma jam'iyyar APC a martaninta yaba wa tsohon shugaban ta yi.
    Sai dai ta ce ba duka abubuwan da ya fadi ba ne a wasika ta yarda da su, musamman game da jam'iyyar da kuma gwamnatin Najeriya.
    Sakataren yada labaran jam'iyyar Malam Bolaji Abdullahi ya ce "ba gaskiya ba ne yadda tsohon shugaban ya yi watsi da tsarin jam'iyyun kasar duka.

2019: 'Batun tazarce ba shi ne a gaban Buhari ba'


  1. Ministan ya ce hauhawar farashin kayayyaki ya ragu da kashi 15 cikin 100 a watanni 11 a jere

Ministan yada labaran Najeriya Lai Mohammed ya ce maganar sake tsayawa takara ba shi ne a gaban Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ba a wani martani da ya yi ga tsohon Shugaba Olusegun Obasanjo.
  1. Ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya aike wa BBC ranar Laraba.
    A ranar Talata ne Mista Obasanjo ya rubuta wata budaddiyar wasika wadda ya ba Shugaba Buhari shawara kan kada ya sake tsayawa takara a zaben shekarar 2019.
    Jami'in gwamnatin ya ce wajibi ne a yaba wa Buhari kan abubuwa biyu cikin ukun da aka yi kamfe a kansu; wato yaki da cin hanci da rashawa da kuma yaki da masu tada kayar-baya.
    Har ila yau, ministan ya ce tsohon shugaban ya ce gwamnatin Buhari ba ta samu nasara ba a fannin tattalin arziki saboda shi ne na uku cikin jerin alkawurran da aka yayin kamfe.
    Daga nan ya ce yana ganin cewa aikace-aikacen Obasanjo ne ba su "ba shi sukunin fahimtar dimbin ayyukan ci gaban da gwamnatin Buhari take gudanarwa ba a halin yanzu musamman a fannin bunkasa tattalin arziki."
    Ministan ya kuma ce dukkan alkalumman da ake amfani da su wajen bayyana karfin tattalin arziki sun nuna cewa Najeriya na samun ci gaba.
    Hakazalika ya ce kasar ta fita daga matsin tattalin arziki ne ta hanyar amfani da shawarwarin da wadansu 'yan kasar suke ba ta.
    Bugu da kari, ministan ya ce hauhawar farashin kayayyaki ya ragu da kashi 15 cikin 100 a watanni 11 a jere.
    Ya ce fito tsarin amfani da asusu na bai daya wato (TSA) ya sa gwamnatinsu ta tara naira biliyan 108 kuma ya ce kasar tana adana fiye da naira biliyan 24 a kowane wata daga sabon tsarin.
    Jami'in gwamnatin ya ce sun samu naira biliyan 120 bayan sallamar ma'aikatan bogi. Haka dai ministan ya yi ta zayyana nasarorin da gwamnatin ta samu daya bayan daya a cikin sanarwar.
  2. Kan batun rikicin manoma da makiyaya ya ce gwamnatinsu a shirye take ta kawo karshen matsalar duk da cewa gadon matasar suka yi daga gwamnatin da ta gabace su, kamar yadda ya ce.
    Daga nan ya bukaci 'yan kasar da su ba su goyon baya don ganin an magance hakan.
    Game da batun tazarcen shugaban kuwa, ministan ya ce da gaske na wadansu 'yan kasar suna kiraye-kirayen neman ya sake tsayawa takara, yayin da wadansu kuma suke nuna adawarsu ga hakan.
    "Muna ganin wannan batun zai iya raba hankalin shugaban a halin yanzu saboda ya dukufa a kowace sa'a don ganin ya magance dimbin matsalolin da suke ci-wa kasar tuwo a karya wadanda galibinsu gadonsu ya yi daga tsoffin gwamnatocin da suka gabata," in ji shi.
    Har ila yau ya ce ba su taba tunanin cewa tsohon Shugaba Obasanjo yana da wata manufa ba kan wasikar bayan ci gaban kasa.
    "Mun karbi shawarwarinsa da zuciya daya kuma muna gode masa kan yadda ya samu lokaci duk da dimbin aikace-aikacen da ke gabansa ya rubuta mana wannan doguwar wasikar," in ji ministan.
    Ita ma jam'iyyar APC a martaninta yaba wa tsohon shugaban ta yi.
    Sai dai ta ce ba duka abubuwan da ya fadi ba ne a wasika ta yarda da su, musamman game da jam'iyyar da kuma gwamnatin Najeriya.
    Sakataren yada labaran jam'iyyar Malam Bolaji Abdullahi ya ce "ba gaskiya ba ne yadda tsohon shugaban ya yi watsi da tsarin jam'iyyun kasar duka.

Saturday, January 20, 2018

Nigeria: An kubutar da turawan da aka sace a Kaduna



An baza jami'an tsaro masu yawan domin neman turawan da aka sace a Najeriya
An baza jami'an tsaro masu yawan domin neman turawan da aka sace a Najeriya
Rundunar 'yan sandan Najeriya ta ce an samu nasarar kubutar da turawan nan hudu da aka sace a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja a makon jiya.
An sace mutanen hudu ne da suka hada da Amurkawa biyu da 'yan kasar Canada biyu a lokacin da suke aikin samar da hasken lantarki ta hanyar amfani da hasken rana a Najeriya.
A ranar Talatar da ta gabata ne aka sace turawan a lokacin da suke hanyarsu ta zuwa Abuja daga Kaduna.
An shiga neman turawan ne gadan-dagan jim kadan bayan sace su, inda aka tura jami'an tsaro da suka hada da sojoji da 'yan sanda da kuma wani jirgi mai saukar ungulu cikin daji domin neman turawan.
Kwamishinan 'yan sanda ta jihar Kaduna, ya shaida wa BBC cewa, an kubutar da turawan ne a wani daji bayan da wadanda suka sace su suka gudu suka bar su a wajen, amma kuma an yi nasarar kama daya daga wadanda ake zargi da sace turawan
Yanzu haka dai an duba lafiyar turawan.

Wasu 'yan bindiga ne dai suka yi wa jerin gwanon motocin turawan kwantan bauna a wani daji dake da nisan kilomita 200 daga Abuja babban birnin tarayyar Najeriya.
Rundunar 'yan sandan jihar ta ce an kashe 'yan sandan Najeriya biyu da ke bawa turawan kariya a lokacin satar turawan .
Satar mutane don neman kudin fansa na dada kamari a Najeriya, a dai-dai lokacin da kasar ke fama da rikicin Boko Haram da matsin tattalin arziki mafi tsanani a shekaru da dama.
Kuma Jihar Kaduna na daga cikin sassan kasar da suka fi fama da sace-sacen mutane don neman kudin fansa.
Ko a watan Fabrairun bara an taba sace wasu Jamusawa guda biyu, kafin daga bisani aka sake su. Haka ma a watan Oktoban da ya gabata an sace wasu Turawan Birtaniya a yankin Neja Delta inda aka saki uku, bayan an kashe daya daga cikinsu.

Nigeria: An kubutar da turawan da aka sace a Kaduna



An baza jami'an tsaro masu yawan domin neman turawan da aka sace a Najeriya
An baza jami'an tsaro masu yawan domin neman turawan da aka sace a Najeriya
Rundunar 'yan sandan Najeriya ta ce an samu nasarar kubutar da turawan nan hudu da aka sace a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja a makon jiya.
An sace mutanen hudu ne da suka hada da Amurkawa biyu da 'yan kasar Canada biyu a lokacin da suke aikin samar da hasken lantarki ta hanyar amfani da hasken rana a Najeriya.
A ranar Talatar da ta gabata ne aka sace turawan a lokacin da suke hanyarsu ta zuwa Abuja daga Kaduna.
An shiga neman turawan ne gadan-dagan jim kadan bayan sace su, inda aka tura jami'an tsaro da suka hada da sojoji da 'yan sanda da kuma wani jirgi mai saukar ungulu cikin daji domin neman turawan.
Kwamishinan 'yan sanda ta jihar Kaduna, ya shaida wa BBC cewa, an kubutar da turawan ne a wani daji bayan da wadanda suka sace su suka gudu suka bar su a wajen, amma kuma an yi nasarar kama daya daga wadanda ake zargi da sace turawan
Yanzu haka dai an duba lafiyar turawan.

Wasu 'yan bindiga ne dai suka yi wa jerin gwanon motocin turawan kwantan bauna a wani daji dake da nisan kilomita 200 daga Abuja babban birnin tarayyar Najeriya.
Rundunar 'yan sandan jihar ta ce an kashe 'yan sandan Najeriya biyu da ke bawa turawan kariya a lokacin satar turawan .
Satar mutane don neman kudin fansa na dada kamari a Najeriya, a dai-dai lokacin da kasar ke fama da rikicin Boko Haram da matsin tattalin arziki mafi tsanani a shekaru da dama.
Kuma Jihar Kaduna na daga cikin sassan kasar da suka fi fama da sace-sacen mutane don neman kudin fansa.
Ko a watan Fabrairun bara an taba sace wasu Jamusawa guda biyu, kafin daga bisani aka sake su. Haka ma a watan Oktoban da ya gabata an sace wasu Turawan Birtaniya a yankin Neja Delta inda aka saki uku, bayan an kashe daya daga cikinsu.

Sunday, January 7, 2018

Sabon rikici ya barke a Taraba


Al'amarin ya faru ne a karamar hukumar Lau, da Katibu da kuma sauran kauyukan da ke kewaye da yankin.

Al'amarin ya faru ne a wasu yankunan karamar hukumar Lau, da Katibu da kuma sauran kauyukan da ke kewaye da yankin.
Wani mazaunin yankin ya shaida wa BBC cewa, "Wasu mutane ne da ake zargin Fulani ne suka kai harin da yin harbe-harbe da kuma cinna wa gidajen jama'a wuta".
"Yanzu haka muna da mutane 25 da aka kashe ban da wadanda suka gudu amma aka bi su a kan mashin aka harbe".
Mai magana da yawun rundunar 'yan sandan jihar David Simal ya tabbatar wa BBC faruwar lamarin.
Ya kuma kara da cewa, "An fara kai harin ne tun ranar Juma'a, kuma ko ranar Asabar ma mutum hudu ne suka rasu ranar Lahadi kuma mutane da dama ne suka mutu, amma kawo yanzu ba za mu iya tabbatar da adadinsu ba".
"An samu mutanen da suka jikkata kuma tuni aka garzaya da su asibi". In ji kakakin rundunar.
Zaman dar-dar na sake karuwa a yankunan na jihar Taraba, sakamakon rikice-rikice da hare-hare da ake samu musamman a kwanakin baya-bayan nan




Sabon rikici ya barke a Taraba


Al'amarin ya faru ne a karamar hukumar Lau, da Katibu da kuma sauran kauyukan da ke kewaye da yankin.

Al'amarin ya faru ne a wasu yankunan karamar hukumar Lau, da Katibu da kuma sauran kauyukan da ke kewaye da yankin.
Wani mazaunin yankin ya shaida wa BBC cewa, "Wasu mutane ne da ake zargin Fulani ne suka kai harin da yin harbe-harbe da kuma cinna wa gidajen jama'a wuta".
"Yanzu haka muna da mutane 25 da aka kashe ban da wadanda suka gudu amma aka bi su a kan mashin aka harbe".
Mai magana da yawun rundunar 'yan sandan jihar David Simal ya tabbatar wa BBC faruwar lamarin.
Ya kuma kara da cewa, "An fara kai harin ne tun ranar Juma'a, kuma ko ranar Asabar ma mutum hudu ne suka rasu ranar Lahadi kuma mutane da dama ne suka mutu, amma kawo yanzu ba za mu iya tabbatar da adadinsu ba".
"An samu mutanen da suka jikkata kuma tuni aka garzaya da su asibi". In ji kakakin rundunar.
Zaman dar-dar na sake karuwa a yankunan na jihar Taraba, sakamakon rikice-rikice da hare-hare da ake samu musamman a kwanakin baya-bayan nan




Monday, January 1, 2018

Zan sa kafar wando daya da masu boye fetur — Buhari

Farashin mai daga 'yan bumburrutu na da tsada sosaiShugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, ya ce shi zai yi maganin wadanda suka haddasa tsadar man fetur a fadin kasar.
Shugaban ya dauki alwashin yin haka ne a wani jawabin da ya yi wa 'yan kasar na sabuwar shekarar 2018.
Shugaba Buhari ya nuna bakincikinsa kan wahalar da 'yan Najeriya suka shiga a lokacin bukukuwan Kirsimeti da sabuwar shekara saboda tsadar man fetur wadda ya ce wasu 'yan Najeriya ne suka haddasa ta.
Ya ce shi ba zai lamunci irin wahalar da 'yan Najeriya suka sha ba a lokacin bukukuwan duk da matakan da kamfanin man fetur na kasar (NNPC) ya dauka na samar da mai a wuraren ajiyan mai.
Shugaba Buhari ya lashi takwabin gano musabbabin yi wa 'yan Najeriya gabadaya abin da ya kira ci-da-ceto.

Ya kara da cewar shi zai hana ko wacce kungiya da ta haddasa matsalar damar iya sake haddasa ta.
A karshen shekarar da ta gabata ne dai Najeriya ta fara fuskantar tsadar man inda babu mai a mafi yawan gidajen mai kuma masu sayar mai din suke sayar wa kan farashin da ya dara naira 145 da gwamnati ta amince da shi.
Wannan ya janyo ce-ce-kuce tsakanin gwamnatin Najeriya da kungiyar dillalan man fetur ta kasar.
Wasu rahotanni sun ce an samu tsadar man ne saboda tsadar danyen mai a kasuwar duniya wadda ta sa kudin man fetur ya zama naira 171 kan ko wane lita, yayin da kudin da gwamnatin kasar ta amince a sayar da mai bai wuce naira 145 ba.
Tsadar mai ka iya sa tsadar rayuwa ta ta'azzara

Zan sa kafar wando daya da masu boye fetur — Buhari

Farashin mai daga 'yan bumburrutu na da tsada sosaiShugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, ya ce shi zai yi maganin wadanda suka haddasa tsadar man fetur a fadin kasar.
Shugaban ya dauki alwashin yin haka ne a wani jawabin da ya yi wa 'yan kasar na sabuwar shekarar 2018.
Shugaba Buhari ya nuna bakincikinsa kan wahalar da 'yan Najeriya suka shiga a lokacin bukukuwan Kirsimeti da sabuwar shekara saboda tsadar man fetur wadda ya ce wasu 'yan Najeriya ne suka haddasa ta.
Ya ce shi ba zai lamunci irin wahalar da 'yan Najeriya suka sha ba a lokacin bukukuwan duk da matakan da kamfanin man fetur na kasar (NNPC) ya dauka na samar da mai a wuraren ajiyan mai.
Shugaba Buhari ya lashi takwabin gano musabbabin yi wa 'yan Najeriya gabadaya abin da ya kira ci-da-ceto.

Ya kara da cewar shi zai hana ko wacce kungiya da ta haddasa matsalar damar iya sake haddasa ta.
A karshen shekarar da ta gabata ne dai Najeriya ta fara fuskantar tsadar man inda babu mai a mafi yawan gidajen mai kuma masu sayar mai din suke sayar wa kan farashin da ya dara naira 145 da gwamnati ta amince da shi.
Wannan ya janyo ce-ce-kuce tsakanin gwamnatin Najeriya da kungiyar dillalan man fetur ta kasar.
Wasu rahotanni sun ce an samu tsadar man ne saboda tsadar danyen mai a kasuwar duniya wadda ta sa kudin man fetur ya zama naira 171 kan ko wane lita, yayin da kudin da gwamnatin kasar ta amince a sayar da mai bai wuce naira 145 ba.
Tsadar mai ka iya sa tsadar rayuwa ta ta'azzara