spon

Saturday, April 14, 2018

Saraki ko Kwankwaso: Wa zai iya ja da Buhari a APC?

An zabi Muhammadu Buhari ne bisa alkawarin samar da tsaro da yaki da cin hanci da rashawa
Masu iya magana kan ce "sawun gwiwa ya take na rakumi" a duk lokacin da suka yi kokarin kwatanta karfin wani abu ko mutum kan abokan karawarsa, da kuma nuna yadda ya yi musu fintinkau ko kuma zai iya share su ya wuce ba tare da wata matsala ba.
Irin wadannan kalaman su ne suka rinka fitowa daga bakin wasu magoya bayan Shugaba Muhammadu Buhari jim kadan bayan da ya sanar da aniyarsa ta fito takara a zaben 2019 domin yin tazarce.
Masu irin wannan ra'ayi na ganin cewa ba wai kawai a jam'iyyar APC ba, har ma a sauran jam'iyyun kasar, babu wanda zai iya ja da shugaban, kuma duk wanda ya yi yunkurin hakan, to ba zai kai labari ba.
Wannan ya kara fitowa fili bayan da a hirarsa da BBC, Sakataren jam'iyyar na kasa, Alhaji Mai Mala Buni, ya ce sun yi farin ciki matuka da fitowar shugaban, kuma da ma abu ne da suka dade suna jira.
Ko ba komai, wasu za su fassara kalaman nasa a matsayin nuna son kai, da kuma hasashen cewa ba za a yi wa sauran 'yan takara adalci ba. Duk da cewa kawo yanzu babu wanda ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar a cikin 'ya'yan jam'iyyar.
Sai dai an dade ana hasashen cewa akwai wadanda suke shinshina kujerar ta Shugaba Buhari. Kuma wasu na ganin za su iya yin kukan-kura su fito ko da kuwa za a dora musu karan tsana - kuma ba za su kai labari ba.
Irin haka dai ya taba faruwa ga tsohon mataimakin Shugaban kasar Alhaji Atiku Abubakar, wanda ya kalubalanci Goodluck Jonathan a jam'iyyar PDP a 2011, duk da cewa Mr Jonathan din shi ne shugaban kasa kuma yana samun goyon bayan shugabanni da gwamnonin jam'iyyar.
Wa zai iya kukan-kura a APC
Jam'iyyar APC dai jam'iyya ce ta hadaka - kuma akwai bangarorin da suke ganin ana mayar da su saniyar-ware a tafiyar da ake yi.
Alal misali ana ci gaba da takun-saka tsakanin 'yan tsohuwar jam'iyyar PDP da kuma wasu 'yan majalisun tarayya da gwamnati a gefe guda.
Abin da ya sa ake ganin 'yan majalisar na kokarin sauya fasalin tsarin zaben kasar domin nema wa kansu mafita, amma sun ce suna yi ne domin inganta tsarin dimokuradiyya

Sanata Bukola Saraki

Wasu na ganin Bukola Saraki ka iya taka wa Buhari burki Ana ganin Shugaban Majalisar Dattawa kasar Sanata Bukola Saraki zai iya kalubalantar Shugaba Buhari, ko da yake a halin yanzu ya musanta hakan.
Amma a baya sau biyu yana neman tsayawa takarar shugabancin kasar.
Gogaggen dan siyasa ne kuma yana da goyon baya a tsakanin 'yan majalisun kasar na APC da kuma PDP.
Babban kalubalen da zai fuskanta shi ne irin bakin jinin da ya ke da shi a tsakanin magoya bayan Shugaba Buhari, wadanda suke ganinsa a matsayin wanda yake adawa da shugaban.
Duk da cewa Sanata Saraki ya sha musanta hakan.
Na kusa da shi na korafin cewa ba a tafiya da shi yadda ya kamata duk da rawar da ya taka wurin kafa jam'iyyar APC da kuma samun nasarar Shugaba Buhari.
A don haka ake ganin zai iya neman kujerar shugaban, ko kuma ya fice daga jam'iyyar.

Sanata Rabi'u Musa Kawankwaso

Har ila yau, a zauren majalisar dattawan kasar, akwai Sanata Rabiu Musa Kwankwaso wanda shi ma ya taba neman shugabancin kasar a 2015 amma Buhari ya kayar da shi a zaben cikin gida na APC.
Ko da yake a wannan karon bai bayyana aniyyarsa ba tukunna, amma alamu na nuna cewa har yanzu bai hakura ba, kuma watakila ya kara gwada sa'arsa.
Tsohon gwamnan jihar Kanon shi ne ya zo na biyu a zaben fidda gwani na 'yan takarar neman shugabancin a jam'iyyar APC a zaben 2015.
Ya ci gaba da yada akidarsa ta Kwankwasiyya a ciki da wajen Kano. Sai dai ba shi da karbuwa sosai a Kudancin kasar, abin da ake ganin zai iya ba shi matsala.
Haka zalika rikicin da yake yi da mutumin da ya gaje shi, Gwamna mai ci Abdullahi Umar Ganduje, ya sa karfinsa ya ragu a jam'iyyar a jihar Kano.
Wasu na ganin zai iya yin kukan-kura ya kalubalanci Buhari ko dan ya nuna karfin imaninsa ga tsarin dimokuradiyya.

Ko za su kai labari?

Masana da dama na ganin fitowar Buhari ta rufe kofa ga sauran 'ya'yan APC, ko kuma ba za su iya kai labari ba ko da sun fito.
Duk wani dan siyasa da yake neman takara a jam'iyyar APC yana bata wa kansa lokaci ne kawai matukar Shugaba Buhari ya fito, a cewar Malam Jafar Jafar, wani mai sharhi kan harkokin siyasar Najeriya.
Ya ce: "... babu makawa jam'iyyarsa shi za ta tsayar a zaben 2019."
Malam Jafar ya ce zabin da ya rage masu muradin yin takara a jam'iyyar APC shi ne kawai su sauya jam'iyya.
Ya kara da cewa "Ga jam'iyyu nan da yawa. Idan dai ba a yi murdiya ba a zaben 2019, akwai yiwuwar jam'iyyar APC za ta iya faduwa zabe."
"Saboda a gaskiya farin jinin jam'iyyar da na Shugaba Buhari ya ragu sosai."
Mai fashin bakin ya ce abin da ya sa manyan 'yan siyasar kasar ba su fito sun bayyana aniyarsu ta takara ba, "shi ne kamar wata dabara ce suke don su fito tashi guda idan lokacin fara yakin neman zabe ya yi."
'Yan kasar dai sun zuba ido su ga jerin mutanen da za su fito su bayyana aniyarsu ta neman kuri'unsu musamman bayan da Shugaba Buhari ya bayyana tasa aniyar.
Wata mai goyon bayan Buhari na sumbatar hotonsa da aka manna
Bayani kan Shugaba Muhammadu Buhari a takaice:
Wata mai goyon bayan Buhari na sumbatar hotonsa da aka manna
  • Shekararsa 72
  • An zabe shi a matsayin shugaban kasa a zaben 28 ga Maris 2015
  • Ya yi shugaban mulkin sojan Najeriya daga 1984 zuwa 1985
  • An hambare shi a juyin mulki
  • Ya samu shaidar rashin kare hakkin dan adam
  • An yi amanna ba shi da cin hanci da rashawa
  • Mai ladabtarwa ne - a kan sa ma'aikatan gwamnati tsallen kwado idan suka yi lattin zuwa aiki
  • Musulmi ne daga arewacin Najeriya
  • Ya tsallake rijiya da baya a wani hari da Boko Haram ta kai masa

 


 




Ko Cristiano Ronaldo karami na iya gadon mahaifinsa?

Shekarar Cristiano karami bakwai kacal amma har ya fara nuna bajinta
Idan har Ronaldo zai iya yin haka, to za a iya cewa dansa ma zai iya yin hakan.
Cristiano Ronaldo dai ya kasance dodon raga a rayuwarsa ta tamaula.
Dan wasan na Portugal mai shekara 33 yana cin kwallaye 50 duk kaka a Real Madrid a cikin shekara tara da ya shafe a kulob din, kwazon da wani bai taba yi ba.
A yayin da a yanzu ake ganin Ronaldo ya kai karshen ganiyarsa, mutane sun fara tunanin yadda duniyar tamaula za ta kasance ba tare da CR7 ba.
Ko yaya kwallon kafa za ta kasance ba tare da daya daga cikin 'yan wasan da ba a taba ganin irinsu ba?
To sai dai da alama dan wasan da ya lashe Ballon d'Or har sau biyar yana kokarin ganin ya samu wanda zai gaje shi ta hanyar dansa, Cristiano karami.
Duka shekarunsa bakwai, amma matashin Ronaldon ya fara nuna alamun kwarewa da kwazo.
Kuma idan aka yi la'akari da cewa yana samun horo ne na musamman daga mahaifinsa, to ba abin mamaki ba ne.
Ku dube shi a nan a tsakanin masu tsaron baya inda ya kwanta ya cilla kwallo a raga a lokacin da suke fafatawa a Bernabeu.
An dauki hoton karamin Ronaldon a lokacin da ya kwaikwayi kwallon da mahifinsa ya yi tsalle ya daki kwallon ta baya (acrobatic) a wasan Real Madrid da Juventus a gasar zakarun Turai.

Cristiano Karami lokacin da ya raka babansa karbar kyautar Ballon d'Or Duk da cewa bai yi nasarar cin kwallon ba da ganin yadda ya dake ta, amma duk da haka Cristiano karami na kokarin tabbatar da ya gaji yadda mahaifinsa ke cin kwallaye.
Kuma ko a yanzu Cristiano karami ya nuna yana samun kwarewar da sannu a hankali za ta iya yin daidai da ta mahaifinsa.
Cristiano Ronaldo karami yana da wasu halaye da kwazo da fasaha irin na mahaifinsa.
Yana motsa jiki da horo sosai. Kuma ya kan yi hakan tare da mahaifinsa.
"Baba, ina son na kasance kamarka," kamar yadda Ronaldo ya taba rubutawa tare da wallafa hotonsa da na dansa a shafin Instagram suna nuna damatsa.
Mun gama shan ice cream, yanzu sai kuma aiki," kamar yadda Ronaldo ya wallafa a Instagram.
Ronaldo gwani ne a bugun fanareti a kwallon kafa, inda ya ci kwallo 100 a shekarun rayuwarsa a tamaula, don haka shi ne ya dace ya horar da dansa dabaru da koyon cin kwallo a raga.
Ronaldo ya shaida wa dansa cewa "Idan ka gaza cin kwallo, sai ka kara kwazo," a yayin da yake koya ma sa dabarun cin fenareti.
Karamin Ronaldon ya barar da fanareti biyu daga cikin uku da ya buga a gaban mahaifinsa.
Bayan cin kwallo kuma, Karamin Ronaldo ya kwaikwayi yadda ake murnar cin kwallo a raga.
A kullum dai 'yan wasan kwallon kafa suna nuna kimarsu ko a bayan fili, inda ake ganin suna saka tufafi masu tsada da motoci masu tsada.
Tuni Cristiano karami ya san dadin zama a cikin mota mai tsada da ta kai fam miliyan 2.15.
Kuma a kallum yana son yin hoto da mahaifinsa tare da sanin muhimmancin sanya tufafi masu tsada
Yanzu kalubalen da ke gaban Cristiano karami kafin ya kamo mahafinsa, shi ne lashe kyautar Ballon d'Or sau biyar tare da girke mutum-mutuminsa kamar yadda aka karrama mahaifinsa.

Friday, April 13, 2018

Real Madrid Za Ta Kara Da Bayern Munich


Real Madrid za ta kara da Bayern Munich a gasar zakarun Turai. yayin da Liverpool za ta kara da Roma.

Za a yi wasannin a ranakun 24/25 na watan Afrilu, sai zagaye na biyu a ranakun 1/2 ga watan Mayu.
Arsenal za ta kara da Atletico Madrid a wasan dab da na karshe na gasar Europa, yayin da Red Bull Salzburg za ta fafata da Marseille.
Za a buga wasan karshe na gasar zakarun Turai a birnin Kiev, na Ukraine, ranar 26 ga watan Mayu.
Yayin da za a yi wasan karshe na Europa a birnin Lyon, na Faransa, a ranar Laraba, 16 ga watan Mayu



Real Madrid ta fitar da Juventus a wasan dab da na kusa da na karshe, yayin da Roma ta fitar da Barcelona.
Ita kuwa Liverpool ta doke Manchester City, sai Bayern da ta yi waje da Sevilla.
A bara ma Real, wacce ke rike da kanbun, ta fitar da Bayern a kan hanyarta ta lashe gasar.
Bayern na kokarin lashe gasar a karon farko tun shekarar 2013.
Bayern ce za ta karbi bakuncin wasan farko, yayin da Roma za ta ziyarci Liverpool a wasan farko.

Monday, April 2, 2018

Buri Na In Taimaka Wa Al’umma Ta Hanyar Fina-Finai Masu Ma’ana – Asabe Madaki

ASABE Madaki, jarumar fim din ‘There is a Way’ da kuma sabon fim din ‘Sarauniya’, ta bada shawarar cewa ya kamata mu yi finafinai da Turanci don mu bada labarin al’adar mu da kan mu. Haka kuma ta fadi yadda a matsayin ta na lauya ta maida hankalin ta ga fitowa a finafinai.

Asabe kwararriyar lauya ce wadda ta ke da matsayin digiri na biyu kuma a yanzu ta na koyarwa ne a bangaren karatun aikin lauya din. Sai dai duk da matakin da ta kai na karatu da aiki a halin yanzu ta samu kan ta a cikin harkar fim, har ma ta fita a finafinai masu dama a Kannywood. Kwanan baya, wakilin mu ya hadu da Asabe a wajen daukar wani fim na Turanci mai suna ‘This is the Way’. Fim din ya na cikin jerin finafinai na Turanci da Kabiru Musa Jammaje ya ke shiryawa.

ASABE Madaki, jarumar fim din ‘There is a Way’ da kuma sabon fim din ‘Sarauniya’, ta bada shawarar cewa ya kamata mu yi finafinai da Turanci don mu bada labarin al’adar mu da kan mu. Haka kuma ta fadi yadda a matsayin ta na lauya ta maida hankalin ta ga fitowa a finafinai.

Asabe kwararriyar lauya ce wadda ta ke da matsayin digiri na biyu kuma a yanzu ta na koyarwa ne a bangaren karatun aikin lauya din. Sai dai duk da matakin da ta kai na karatu da aiki a halin yanzu ta samu kan ta a cikin harkar fim, har ma ta fita a finafinai masu dama a Kannywood. Kwanan baya, wakilin mu ya hadu da Asabe a wajen daukar wani fim na Turanci mai suna ‘This is the Way’. Fim din ya na cikin jerin finafinai na Turanci da Kabiru Musa Jammaje ya ke shiryawa.



Kannywood: Ni Da Sake Yin Aure Ba Yanzu Ba – Inji Fati Kk

Tun ba yau ba ake rade-radi kan mutuwar auren ta wanda ya sanya har ta kwaso kayanta daga Kano zuwa Kaduna, garin iyayenta.Auren ta na biyu da tsohon mijinta wanda yayi sanadiyar komawar ta Kano, Allah ya albarkace su da yara biyu,Ahmed da Yasmin.

A hirar ta da wakilin jaridar Leadership Ayau, Fati KK ta fayyace masa labarin dalla-dalla kan yadda al’amura suka kasance har suka rabu da mijinta.

“To ni dai abin da zan iya cewa, ni dai har ga Allah ya sani, wadanda muke tare da su su ma sun sani, na so zaman aure.In da ba na son zama da shi, wallahi ba zan mike kafafu na yi ta zuba ‘ya’ya ba. Na fuskanci gori daban-daban duk na shanye, kuma hakan bai sa ni bijirewa ba har na ce a sake ni ba, na kan zauna in yi kuka, watarana sai na fada masa, sai na gane in har wani ya ki ka, ai Allah na son ka. Na fuskanci kalubale kala-kala, sai dai in ce mun gode Allah.”

Jarumar wacce aka daina jin duriyarta a fagen shirya fim bayan auren ta ta bayyana cewa dangin mijinta sun zargi ta da bijire ma mijinta bayan ta samu labarin cewa zai kara aure. Tace basu fahimce ta ba domin bata da kishin samun kishiya. Haka zalika bazata zabi rabuwa da mijinta kan matsalar rashin kudi/talauci.

“Mun haihu da shi yara biyu, Abu ya ki ci, ya ki cinyewa, a gaskiya talauci bai taba sa na ce zan rabu da wanda nake tare da shi ba. Na dai samu surutai a cikin danginsa, wai don zai kara aure ne na bijire masa na ce ya sake ni, alhalin wallahi tallahi, wallahi tallahi, wallahi tallahi ban san wannan zancen ba, ban ma taba jin sa ba. ”

Kannywood: Babu Mace Mai Dadin Zaman Aure Kamar ‘Yar Fim – Ladidi


A duk lokacin da aka dauko batun aure, wasu da yawa kan yi wa ‘yan fim gani-gani. To amma a wannan karon magana ta kare, domin jarumar da muka tattauna da ita a wannan makon ta ce rashin sani ne ke sa mutane kyamatar auren ‘yan fimIdan mutum ya fahimci lamarin kuwa, zai fi wadanda ke auren wadanda ba ‘yan fim ba jin dadin zaman aure, ko me ya sa?

Sammam Masu karatu ko kun san shahararriyar jaurmar wasan kwaikwayon ta taba yunkurin shiga aikin soja kafin ta fara wasa?

A karanta firar duka a Taurarin Nishadi
Muna so mu ji cikakken tarihin rayuwarki
Ni dai sunana Ladidi Abdullahi An fi sani na da suna Tubeeless. An haife ni a Kaduna a wata unguwa da ake kira Sabon Gari Nassarawa, wato dirkania ke nan. Na yi Furamare wato a Nassarawa na kuma je makaratar gaba da Furamare.duk a Kaduna wato, ina gama sakandare aka yi min auren fari sai Allah bai yi zamana da mijin ba, sai muka rabu.




Daga nan sai na ji ina son yin aikin kaki, na je na sayi ‘form’ din aikin soja na ruwa na cika na ba da aka kira mu, na je duk abubuwan da ake yi na yi daga, baya ban sake bin ta kan shi kuma ba saboda oda wasu dalillai.

Yaushe kika fara fim din Hausa, da wane fim kika fara, kuma Me ya jawo ra’ayinki kika shiga?

Wata rana sai Rabi’u Rikadawa ya zo gida ya same ni ya ce min, ki zo mu je ki yi aikin fim, shi da Obina. Na ce musu ku je zan zo,
Amma sai na ki zuwa na neme su. Sai muka hadu da Zainab Abubakar muna hira ta ce min, ki zo mu yi aikin fim mana. Na ce mata zan bi ki. Ta ce, min, duk ran da za ta yi aikin za ta kira ni mu je mu yi tare. Na ce mata ba damuwa. kuma kafin nan, muna Hausa ‘drama’ a makaranta dama. Ran da Alfa ‘care’ zai yi wani fim sai ta ce na zo mu je.

Na ce mata to, muka je muka gana, sai shi ya tambaya da ma ina fim ne?

Saboda ya ga ba na kuskure. Daga nan sai na muka cigaba da zuwa N TA. Oganmu George ya ce,, na iya ‘drama’ ana ta sani. Daga nan kuma ’yan Kano suka zo Kaduna za su yi wani flm sai aka kira ni. Kafin nan mun yi wani flm wanda Rabi’u Koli ya sa Wada Rikadawa ya kira na yi, sai na ciga da aiki sai aka cigaba da kira na ina yi, shi ne. Sai dai na manta shekarar gaskiya. Nasiru Gwagwazo zai yi wani fim Balarabe da Balarabe dila ya kira ina Abuja ya ce na je Kaduna za mu yi wani fim. Shi ma Nasiru Gwagwazo ya kira ni, na ce musu ina zuwa nako zo muka yiFim din da na fara na Turanci ne, shi ne na Alfa ‘care’.