spon

Monday, July 23, 2018

Home ZAWARCI Complete Book

Subscribe Our Channel


*K*wance take a tsakar ɗaki sai muɗiɗɗiƙa take a ƙasa, yunwa kawai take damunta, ga kudaje sun cika ɗaki kamar toilet in daya shekara bai samu wanki ba,,,,, wasu zafafan hawaye suka zubo mata masu zafin bala"i, a bayyane tayi magana , wayyo Allahna, da ina can naci mai kyau , babu ruwana da wata yunwa ko ganin ƙazanta,,,, goge hawaye tayi da bayan hannu lokacin da taji mahaifiyarta tana kiran sunan ta,,,,,

*R*aihana baki ji na ne?""" umma ina zuwa, tsaki tayi , sannan tace idan ma baza ki zo, kin huta, dama wankau ne, aka kawo sunce yau suke so, idan zakiyi to kizo ki karɓa, idan kuma bakya yi ki faɗa masu, a daidai lokacin da ta fito a tsakar gida,,,,,,,

*T*ashin kayan wankin ta gani, ta gyara ɗaurin zaninta, sannan tace umma zanyi, umma ta kace da dariya, sannan ta taɓa hannu, tace yo kice ma baza kiyi ba, zama raihana tayi a ƙasa ta jayo wanki ta fara irgawa, sannan ta kalli yaron tace to wankin na ɗari da hamsin ne, yaron yace Eh, tace ga kuɗin, ya miƙa ma raihana ta ƙarba, tace bayan la"asar ka dawo ka ɗauka yace to yace sannan ya fita daga gidan,,,,,,,,,,,,,,

Umma tace to yanxun dai kafin ki fara wannan wanki, ki fara wanke kayan babanki sannan, raihana tace tou umma,

��������
������
*ZAWARCI*
��������
������
Saida ta wanke kayan babanta kala biyu, sannan ta fara wankin kayan wankau, yinin ranar nan haka ta yini ta wanke kaya,,,,,,

Lokacin da ta gama wankin hijabinta data gama koɗewa ta jawo daga saman iyiga, ta rataya a wuyanta ta fita tabar gidan............

Tana fita umma tayi dariya tace munafikar Allah, ai tunda dai *zawarci* kika zaɓa sai kixo mu zauna kice uwar da nake a gidan,,,,,,,,,

Raihana tana fitowa wani shago taje, suka gaisa da mai shagon, bayan sun gama gaisawa tace don Allah fulawa za"a bata kwata ɗaya, yace to, ya ana mata, tace don Allah ka bani bashin manja na hamsin insha Allah zan kawo maka , yace gaskiya raihana bakya san biyan bashi wallahi, tace kayi haƙuri wallahi zan kawo maka dana samu, shamsu yace, baia san ranar samu ba kenan,

Idan zaka bani kawai ka bani idan baza ka bani ka faɗa man, gaskia bazan bayar ba, tace to yanxn naji magana, ta ɗauki fulawarta da canjin ishirin ɗinta ta fito daga shagon,,,,,,,,

Sallama tayi ta shigo cikin gidan, matar babanta da ta dawo daga unguwa tace ina kika je ne?""""raihana tace fulawa na siyo gwaggo, cikin tashin hankali gwaggo tace waye ya baki kuɗi?""" tace nayi wankyau ne, tsaki tayi sannan taje inda fulawar take ta ɗauketa, tace wallahi saidai a ajiyeta da safe ayi fanke kowa ya samu, raihana tace gwaggo nifa nayi wankin nan na samu kuɗina gwaggo tace koma uwarki tayi haka za"ayi, ta ɗauke fulawar ta shige , cikin ɗakinta,,,,,,,

����
*zawarci*
����

Bayan ta ɗauki fulawar ta shige cikin ɗaki raihana ta miƙe ta nufi ɗakinsu, kwanciya tayi saboda tun safiya bata ci komai ba, ga azabar yunwa dama tana ji kuma tayi wanki har ta gaji, kuma hdama kowa dai yasan wankindasa jin yunwa,,,,,,

Raihana wasu hawaye suka zubo nata , abinda ta fara tunawa, hango tsareren gidanta, tayi da tsaruwarsa da kuma yanda yake a tsabtace, cikinta ta laluba, lokacin data tuna irin abincin da take ci, uhum Allah sarki rayuwa tace,

Tashi tayi ta fito tsakar gida dan ganin waye yake sallama, wai ance a bada wanki, raihana tace to ɗauki gashi can , ya nufi wurin data nuna mashi ya nufi wurin yana cewa wai mama tace a kawo maki kaɗin taliya?"

Zainaba tace a,a, banda hali, gwaggo data ke alwalla tace kaje kace a kawo, kumin dare tayi ta, yace to, ɗakar wankin yayi ya tafi,,,,,,,,

Gwago tace dan rashin imani ubanki yana can yana fama liƙewa mutane takalmi baza ki tausaya mashi ba?" wai mutum ya haifeka amma kana masa hassada, raihana tayi tsaki ta shige ɗakin su.........



����������
*ZAWARCI*
��������

Gwaggo tace uwarki da ita kike tsaki, shegiyar nan, idan kinki haushi ki fitar da miji kiyi aure,,,,,,,,,
[07:24, 08/11/2017] ‪+234 813 308 2423‬: ����������
��������
������
����
*ZAWARCI*
����������
��������
������
����

*page* 2⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ��✍��

*JAMEELA MUSA*

����������
��������
������
����
�� *ZAWARCI*

*A* ɗaki rahaina tayi magana ƙasa ƙasa, tace wallahi ba uwata nayi ma tsaki ba, kuma maganar aure, idan Allah ya kawo man lokaci sai inyi,,,,,,

*U*mma kiyi mata magana ta bani fulawata yunwa nake ji taliya zan kaɗa inci da manja, raihana ce take ma mahaifiyarta magana,,, umma tace bazan mata magana ba, dana ce kada ki kashe aurenki ai cewa kikai ke ba"a sanki, to yanxun ana sanki sai ki zauna kiyi ta haƙuri tunda haka kika zaɓarma rayuwarki,,,, raihana tace umma haka zaki ce?"" Eh haka nace kuma haka ne,,,, uhum raihana tace sannan ta ɗauki buta ta fita daga ɗakin,,,,

��������
*zawarci*
����������
*R*aihana ta kalli wani jikan gwaggo da yake zaune yana cin abinci, da sauri taje inda yake, robar ta ɗauka ta zubar da abincin a ƙasa, tana faɗin tunda banci babu uban da ya isa yaci ko yasha a gidan nan harsai naci, idan kuwa ba haka wallahi ba"a nemi zaman lafiya ba,,,,,,,,

Yaron da raihana ta ɓare na abinci ya faɗi ƙasa ya fara burgima yana ihu yana ƙarawa, da sauri gwaggo tayo waje tana faɗin lafiya?""" raihana tace ina ma lafiya tunda baki nemi zaman ta ba a gidan nan, gwaggo ta tafa hannuwa tana sallalami , sannan ta riƙe haɓarta tace raihana, yanxun da ni zaki yi faɗa a gidan nan?""" raihana tace Eh, tana magana tana zaro idanuwa, tace udan har baki bani fulawata ba yau saidai gidan nan ya tashi saboda bala"i, gwaggo tayi dariya tayi guda, ayyuri yuriiiiii yuriiiiii, to uwarki ma ta buga dani tabarni danni nan da kika bakan gixo ce, dan idan har hadari ya taru saina tsotseshi,,,,,

Rainaha tace aikin banza wanda bakuyi imani da Allah ba baku da aiki sai neman asiri, kuma idan har ina a gidan nan wannan yaron babu shi babu ƙara cin bacci saidai yunwa ta kasheshi kowa ma ya huta,,,,,,,

Gwaggo ta sake sheƙwa da dariya sannan tace, ke yunwa zata kashe, kuma ni yanxun dana ga dama sai in mayar dashi gudan ubanshi, kuma ubanshi yana da abincin bashi dan ubanshi namiji ba kamar ubanki ba, wanda sai ƙato ya cire takallmi sannan ya wanke, raihana tace Eh a haka aka gani kuma aka aura,

Gwaggo tace lallai yarinya dani kike magana, tunda *zawarci* kika zaɓa haka zamu zauna dani dake a gidan nan aure ko saidai kiga anayi,, tana faɗin haka ta kama hannun jikanta ta shige ɗakin ta,,,,,,,,

Raihana tace karyar banza baƙin bakinki ya faɗa ma jikokinki,,,,,, itama daga nan bata sake magana ba, ta ɗauki butarta ta kona ɗaki,,,,,,,,
��������
*zawarci*
��������
Raihana baki kyauta ba, ummarta take mata magana, tace umma barta, ninan walkice daidai ƙugun kowa, umma tace rufa man baki, tunda kinsan halinta kika biye mata,,, umma tace to wallahi nidai saidai in bar maki gidan nan,

Raihana tace kiyi haƙuri, kada kibar gidan nan saboda ni, umma tace idan kuwa ina san zaman lafiya da tsira da rayuwata dole in tafi dan bana iya zama ina kallon wannan wulaƙancin wallahi,,,,,,,,,

Sallamar babansu raihana , umma taji ta tashi ta fito tana mashi sannu da zuwa, ya amsa cikin kulawa, itama raihana fitowa tayi ta mashi sannu da zuwa, ya amsa sannan yace Allah yayi maki albarka, daga ɗaki gwaggo tace ba amin ba, sannan ta fito tsakar gida taci gaba da cewa kace Allah ya tsine mata albarka, wannan da kake gani, tana nuna rainaha da yatsan ta, tace to wallahi bakai sa"arta ba, saboda lalatattar yarinya, baba ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu, yace bana san irin wannan kalamin daga yau, gwaggo tace dama haka zaka ce tunda an shanye ka sakarai mai matacciyar zuciya, duk gwaggo take wannan maganar , baba bai sake magana ba ya nufi ɗakinshi,,,,, raihana da umma suma ɗaki suka koma,,,,,,,,

������������
*ZAWARCI*
����������

*T*unda asuba, gwaggo ta fito daga ɗaki ta fara jaraba, tana masifa tana zage zage, babu wanda yayi mata magana, taci gaba da cewa idan banda munafircia matsa ma yarinya ta fito da miji tayi aure sai a barta ta zauna, kuma tana da nasu santa, to tunda *zawarcin* kika zaɓa sai kizo ki zauna,

Raihana dai daga ita har umma babu wanda yayi magana , haka ta kari masifarta ta koma ɗaki,,,, ,,,,,

Bayan hantsi ya fito baba ya fito dan tafiya wajen sana'ar sa, kuma gwaggo batayi wannan famke ba, kuma batayi komai da fulawar raihana ba, haka baba ya fita daga gidan baici kuma baisha komai ba,,

Gwaggo bayan fitar baba itama gyalenta ta yafa itama fita tayi tabar gidan,,,,,

Wata maƙociyarsu tayi sallama ta shigo, bayan gaisuwa tace raihana ga dakan tashshi raihana tace to, da ƙarfe nawa kike so?""" tace bayan azahar, to Allah ya kaimu lafiya, nawa za"a bada?"""inji matar, raihana tace tiya nawa ne?"" biyu da rabi ce, raihana tace to ki bada abinda kikai niyya, tace to, ɗari biyar ta ciro ta bawa raihana, tace ta riƙe sauran canji, godiya raihana tayi, matar ta tashi ta fita, itama raihana fita tayi ta nufi shago, gari da suger ta siyo sannan tayo gida............

*zawarci*
[07:25, 08/11/2017] ‪+234 813 308 2423‬: ������������
����������
��������
������
����
*ZAWARCI*
������������
����������
��������
������
����

*page* 3⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ��✍��


*JAMEELA MUSA*

����������
��������
������
����
�� *ZAWARCI*

*S*allama raihana tayi ta shigo gida, umma ta amsa mata, kusa da umma raihana taje ta zauna, garin ta ajiye sannan taje ta ɗauko kofi da cokali, wurin ta dawo ta ɗauki garin ta haɗashi, bayan ta gana , ta miƙawa ummarta tace ummana sha ki rage man, umma tace ni bana sha, raihana tayi juyin duniya tace bazata sha ba,,,,,,,,,,

*R*aihana ta ɗauki garin tasha, bayan ta gama sha ta tashi ta fara dakan tashshin da aka kawo mata,,,,,,,

��������
*zawarci*
��������

*B*ayan raihana ta gama dakan tashshi ta kwashe, bayan ta gama kwashewa ta zauna a wurin tabaryar da tayi dakan tana hannunta, ta jingina kanta da ita, hawaye masu zafi suka zubo mata, ta runtse idanuwanta, abinda ta fara tunawa shine,,,

�� ��
*gidan mijinta*
�� ��

*R*aihana ta fara tunawa, wata rana, da sallama ya shigo gidan ko inda yake bata kallaba, shi kuma cikin farin ciki ya shigo yana faɗaɗa murmushin shi, yace raihana barka da gida, tsaki tayi, ita babu sannu da zuwa kuma bata ansa sallamar ba,,,,,,uhum ajiyar zuciya zainaba tayi sannan a bayyane tayi magana tace rabon *zawarci*

������
*zawarci*
������
Idanuwanta ta sake runtsewa, abinda ta ƙara tunawa, raihana zanyi tafiya, ta sake hango lokacin da ta taɓe baki, sannan tace sai wani magana kake man saman kai babu girmamawa, idan zakayi tafiya ina abinda ya dameni"""",,,,,,, murmushi yayi sannan ya ciro kuɗi har dubu ishirin ya ajiye mata a gabanta,,,,,,,,, wasu hawaye suka ƙara kwararowa daga gudan raihana, tace *astagafurulah*

*zawarci* baiyi ba, abinda raihana ta faɗa kenan, sannan ta gige hawayenta, tace abinda nafi ƙarfi yanxun shine yafi karfina,,,,,,,,,, ***

��������
*zawarci*
��������

*R*aihana ta janye taɓaryar gabanta ta jingina da bango ta mike,,,, a daidai lokacin da gwaggo tayi sallama ta shigo,, raihana ta amsa, gwaggo ta cire gyalenta ta rataya a igiya, sannan tace raihana wani mutum ne a kofar gida yake maki sallama, raihana tace naji, ɗakin ummanta ta shiga, ta ɗauko kwandon wanka, ta duba taga babu sabulu a ciki, tsaki raihana tayi tace kai Allah kasa mu dace, saman window ta duba ta ɗauko wata ledar omo, ta zuba ruwa ta shiga wanka,,,,,,

��������
*zawarci ne*
��������

*T*ana fitowa wanka alwalla tayi ta shige ɗakinsu, umma ina man yake?"" in shafa umma tace babu mai ya ƙare fa, raihana tace yanxun ya zanyi a daidai lokacin da take zama saman tabarma, umma tace ɗauko waccan ledar ina da sauran man gyara ki murza , ajiyar zuciya raihana tayi sannan ta miƙe taje ta ɗauko ta shafa, fuskar nan ta ɗauki ƙalli, da kafafuwanta, kuma babu powder, ta kalli kanta a madubi, tace rayuwa kenan, girgiza kanta tayi hawaye masu zafi suka zubo mata, umma ta kalleta tausayin raihana ya kamata, saboda raihana bata san wahala, amma a fili tace haba har kin gaji?"" ai baki komai ba, lokacin dana faɗa maki kiyi haƙuri ki zauna ai cewa gani kikai gara ki dawo gida,,, haushi ya ishi raihana bata sake magan ba, ta ɗaga ƙasan katifarta ta ɗauko wata ƙoɗaɗɗiyar atamfa tasa, da habar zaninta ta goge fuskarta ta fice daga ɗakin,,,,,,

������
*zawarci*
������
Tana fita umma tace kinga da yanxun kina gidanki kina yin rayuwarki yanda kike so, kinzo ki liƙe nan sai wahala kike sha,,,,,

Fitar raihana wani mutum ta hango tsaye bakin bishiyar kofar gidansu kamar ya fiddoshi daga cikin ƙasa, raihana tayi tsaki sannan ta nufi wurin shi cike da masifa, tana zuwa babu ko gaisuwa tace malam yadai?"" yace nine dama nazo ina sanki, to naji kana do na, sai mi kuma?"" maganar aure ce, raihana tace to daga yau kada in sake ganin ƙafarka nan kaji na faɗa maka?"" tana faɗin haka bata jira abinda zaice ba tayi cikin gida, a zaure ta tsaya, tace banda iskanci da shara da bola dan taƙamar kana *zawarci* kowa sai yaxo, tsaki tayi sannan tace shege ƙazamin banza, ...............


Hhhhhhhhhh
��������
*zawarci*
��������
[15:01, 08/11/2017] ‪+234 813 308 2423‬: ����������
��������
������
����
*ZAWARCI*
����������
��������
������
����

*page* 4⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ��✍��

*JAMEELA MUSA*

����������
��������
������
����
�� *ZAWARCI*

*gargaɗi a bisa wata ƙungiya, da bama buƙatar saka sunan ta, dan haka muna roƙonsu dasu guji juya mana littafi ta ko wace fuska, idan kunnne yaji ���� gangar jiki ya tsira* ����‍♀

��������
*zawarci*
��������

Sallama tayi a daidai ƙofar ɗakin ummanta ta shige, har kin dawo?""" Eh kawai tace, inda ta ajiye tashshin data daka ta wuce ta ɗauka , sannan tace umma zan kai mata saƙon nan, umma tace sai kin dawo , to tace tayi gaba,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,

*zawarci*
Raihaina tana fita umma tace Allah ya baki miji kiyi aure raihana ki huta da wannan rayuwa, ,,,,,,,,

*R*aihana tana fitowa maƙotansu ta shiga, gidan badiyya, sallama tayi ta amsa mata tace raihana ki shigo mana, raihana tace to, ta shiga, ta samu wuri ta zauna, suka sake gaisawa, sannan raihana ta fidda tashshin ta bata, godiya tayi , sannan tace bara inxo,,, fitowa tayi taje kicin ta zubo ma raihana abinci,,,, sannan ta dawo ta ajiye mata, murmushi raihana tayi danma kada a ɓata lokaci kawai tace tana azumi,,,,,,,,,,,,

������
*zawarci*
������
*B*adiyya tace Allah sarki azumin mi kike?"" murmushi raihana tayi tace ramuwa nake, badiyya tace to Allah ya bada lada, amin raihana tace, sallamar mijinta suka ji, raihana tana zaune taga badiyya ta tashi cikin sauri ta fita,,,,, tana kallon ta tana zuwa ta rungumeshi tana oyoo yoo barka da dawowa baban sadiq,,, lader hannun ta ƙarɓa cikin girmamawa tana buɗewa dariya tayi saboda ganin abinda yake cikin ledar , sannan ta matsa kusa dashi ta ɗora kanta saman kafaɗarshi tace na gode Allah ya saka da alkairi ubangiji ya ƙara rufa asiri Allah , amin yace yana murmushi,,,,,,,

*zawarci*

Hmmm ajiyar zuciya raihana ta sauke, sannan ta tuna cewa ita idan mijin nata ya kawo cewa take yaje ya ajiye,,,,,,, a bayyane tace gashi an barni da *zawarci* jiki a sanyaye ta fito tsakar gida, tace nidai zan wuce,,,, �� raihana taga masoya suna soyewa hankalinta ya tashi,,,,,,,, badiyya tace haba tun yanxun?"" don Allah ki bari yanxun zai fita sai muyi fira, raihana tace a, a, ina aikine a gida,,,,,, badiyya tace to ngde, a gaishe man da umma, raihana tace to sannan ta fita tabar gidan,,,,,,,,,

��������
*zawarci*
��������

*A* gida raihana ta shiga ɗakinsu,,,, umma ta samu tsaye ta riƙe hijabinta a hannu, raihana tana shiga umma tace mata yawwa, zanje duba bayi bata da lafiya, raihana tace sai kin dawo a daidai lokacin da take kwanciya saman tabarmar kaba,,,,,,, umma ta fice tabar ɗakin,,,,,,

������
*zawarci*
������

*Raihana* tana kwanciya ta ɗaga kanta sama tana kallon izarar ɗakinsu, wasu hawaye masu zafi suka zubo mata, ajiyar zuciya tayi sannan ta gyara kwanciyarta saman hannun ta na dama,,,,,,,,,,,,,,, abinda ta fara tunawa,,,,

��������
*rayuwarta*
��������

*Khadija* shine ai nahin sunan *raihana* babanta malam ibrahim, da ɗan kasuwa ne, ya ɗan riƙe kuɗaɗe babu laifi, daga baya Allah ya kawo mashi karayar arxiki, matan malam ibrahim biyu, binta itace babbar matarsa wanda suke kira da gwaggo, tana da "ya"ya, basai na tsaya lissafo su ba, halima itace mahaifiyar raihana, wanda suke kiranta da umma, umma ta haihu sosai amma Allah bai bata wasu rayuwa ba sai kan khadija, wanda aka sakawa sunan maman malam ibrahim, yayarta ɗiyar gwaggo itace take kiranta da raihana, saboda haka shine dalilin da yasa kowama ya kekiranta da haka, dan yanxunma sunan ta ya ɓata saidai *raihana*

Gyara kwanciya raihana tayi sannan ta goge hawayen da suka zubo mata,,,,,

��������
*zawarci*��
��������

Ku biyo ni sannu a hankali don Allah donjin labari *zawarci*

Ina maku fatan alkairi masoyana , ku biyo ni sannu a hankali don jin wannan labari, *ameenxi writr's association* a shirye muke wajen ƙawata maku da daɗaɗa maku din farin cikin ku,

*jameela musa* ke cewa ku kasance dani lafiya,,,,,,

07060797938, a shirye nake da jin ƙorafinku ����
[15:02, 08/11/2017] ‪+234 813 308 2423‬: ����������
��������
������
����
*ZAWARCI*
����������
��������
������
����

*page* 5⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ��✍��

*JAMEELA MUSA*

����������
��������
������
����
�� *ZAWARCI*

*gargaɗi a bisa wata ƙungiya, da bama buƙatar saka sunan ta, dan haka muna roƙonsu dasu guji juya mana littafi ta ko wace fuska, idan kunne yaji ���� jiki ya tsira* ����‍♀
������
*ZAWARCI*
������

*B*ayan ta gama goge hawayen da suka zubo mata a ido, ta tashi zaune ta zabga tagumi, sannan ta ɗora kanta saman guiwarta,,,,,

*zawarci*��

Malam ibrahim mahaifin *raihana* shine yayi kyautar raihana ga wani yaronshi mai suna aminu, yana da kirki sosai, ya bashi raihana ne, saboda ya matsa mashi yana santa, shi kuma ya bashi raihana saboda ya yaba da hankalin aminu,,,,,,

*to haka baba ya bawa *aminu* auren raihana, ansha shagali sosai kuma aminu yayi hidima saboda yana san raihana kuma komai zai iya yi, saboda ita idan dai abun baifi ƙarfinshi ba,,,,,,,,

��������
*zawarci*
��������

*Raihana* da sauri ta goge hawayen idon ta dan kiran sunan ta da taji gwaggo tanayi,,,,, ba tare da ta amsa kiran ba, ta tashi ta fito tsakar gida,,, kallo tabi gwaggo dashi har yanxun batayi magana ba,,,,,,,

Gwaggo tace, wallahi tun ɗaxu nake neman wanda zai kai mana niƙa ban samu ba, raihana ta ɗaure fuska sosai sannan tace idan baki samu mai kai niƙa ba sai akayi me?"""" gwaggo tace wannan ɗaure fuskar naki bazai hana ince kije kikai ba, tunda ba"a samu yaron aike ba,,, kam raihana tace, sannan tace lallai gwaggo kinzo da abinda baya yuwuwa, gwaggo tace ai dan zai yuwu nayi magana, saboda haka sai kinje, raihana tace bazanje ba,,,, sallama umma tayi ta shigo gidan, a daidai lokacin da gwaggo take cewa da kina gidan mijinki zanje in kiraki kikai niƙa ne?""""

*t*saki raihana tayi sannan tace aike kina so kiyi man gorin aure, bayan nasan idan lokaci yaxo sai nayi, gwaggo tace wannan kuma matsalarki, dan wallahi idan baza kikai niƙan nan ba, yau bazanyi tuwon nan ba, saidai ubanki ya kwana da yunwa,,,,, umma tace ɗauki kije kikai ɗinƙan kinji,,,,, raihana zatayi magana umma ta dakatar da ita, ta hanyar cewa ba komai wata rana sai labari, gwaggo tace ba labari ba koma b.b.c ne ina ruwana,,,, ta juya ta wuce ɗakinta, inda gwaggo ta ajiye buhun niƙan da kuɗin raihana taje ta ɗauka sannan ta fita daga gidan,,,,,,,,,,

��������
*zawarci*
��������

Raihana sai Allah ya isa take har takai shagon niƙa,,,,, mai niƙan ya kalleta ya bushe da dariya, sannan yace baiwar Allah ke aka aiko?""" rahaina bata yi magana ba, ta haɗa hannuwanta ta rugummesu a ƙirjinta,,, mai niƙan yace ni wallahi da zaki yadda kawai in fito muyi aurenmu in rufa maki asiri tunda shi aminun ya kasa,,, ko inda yake raihana bata kalla ba, dariya yayi lokacin daya ɗaga buhunta ya juye masarar a cikin inji, yaci gaba da cewa matana ukku yarana ishirin da biyar, kallon ƙasa da sama raihana tayi mashi, wata irin dariya yayi sannan yace Allah sarki irin wannan kallo ai sai kisa mutum yayi fitsarin zaune dan daɗi, tsaki raihana tayi ta duƙar da kanta ƙasa har ya gama niƙan,,,, ta ɗuka zata ɗauka da sauri ya riƙe yace bari insa akai maki, raihana ta saki, kuɗin ta miƙa mashi yace tabarsu, yana yashe baki yace wannan toshine, murmurshin baƙin ciki raihana tayi taji kamar zuciyarta zata fashe wato da niƙa za,ayi mata toshi,,, yaronshi yace ya ɗauki niƙan yakai gidansu, yaron ya ɗauka yayi gaba, raihana tafi bayanshi, mai niƙa sai ɗago hannu yake yana cewa sai yaxo cin tuwo anjima,,,

��������
*zawarci*
��������
*raihaina* haka tabi bayan yaron tana zance zuci, lallai waƙƙahi mutumnn nan ya raita mata, hankali, addu"ar ta ɗaya kada yazo gudansu dan babanta yana iya cewa ya turo, tunda dama kullum sai yayi mata maganar tayi aure,,,,, a daidai lokacin da tayi sallama cikin gida,,,,

*zawarci*
Yaron ya ajiye niƙan ya fita, gwaggo ga niƙan nan, to aisai kiyi tankaɗe, raihana tace hada wani tankaɗe, tace E , taci gaba da cewa ai da uwarki ce idan tana aiki baki da zama sai kinga an gama, dariya ryhaina tayi sannan tace maida wuƙaƙen zan maki, a daidai lokacin data shiga ɗakinsu,,, hijabinta ta cire ta miƙawa ummanta kuɗin niƙan tace ki ajiye wannan , umma tace na miye?"" raihana tace nawa ne na baki, umma tace to, bayan ta nashi kuɗin ta fito tsakar gida ta fara kama ma gwaggo aiki,,,,,,,,,

��������
*zawarci*
��������
*W*ani yaro ne ya shigo da tsirin kayan wanki saman kanshi, sallama yayi sannan ya nufi inda raihana take zaune, kama mashi tayi ya sauke, sannan ya miƙa mata kuɗi yace ga kuɗin ruwa da sabulu, ta ƙarba ta ɗaure a haɓar zani tace idan Allah ya kaimu jibi ku dawo ku karɓa, yaron yace to, sannan ya fita daga gidan,,,,,

*zawarci*
Gwaggo tace raihana wannan wanki ma ai babu wani datti sosai, raihana dai bata yi mata magana ba ta ɗauki kayan mutane ta nufi ɗakinsu dashi, bayan ta ajiye ta fito suka ci gaba da aiki,

��������
*zawarci*
��������

Tunda safe gwaggo tazo kofar ɗakin su raihana ta riƙe ƙugu, tana cewa ki fito ubanki babu lafiya ki kawo kuɗin wankin nan inje in siyo mashi magani, daga ɗaki raihana tace wane irin kufi kuma?"" wanda kike tarawa a daidai lokacin da ta yaye labulen ɗakin ta siga ciki, raihana tace to gaskiya banda wasu kuɗin ni da zan bayar, gwaggo tace kina dasu, raihana tace faɗa man abinda nake siyawar, gwaggo tace wanki mana kina nan kin tara kuɗi dake da uwarki kin boye, dariya raihana tayi sannan tace baki son muna tara kuɗi gwaggo?""" tsaki tayi gwaggo sannan ta fita tabar ɗakin,

*zawarci*
Umma tace idan kina da kuɗi ki bata mana, raihana tace barta, zanje wajen baban dakai na, umma tace to, miƙewa raihana tayi ta fita daga ɗakin, ɗakin baba taje ta shiga tare da sallama, ya amsa , kusa dashi taje ta gaishe shi, ya amsa sannan tace baba miye ya sameka??"" baba yace mura nake, amma da sauƙi yanxun zan fita, raihana tace to Allah ya ƙara sawakewa, baba yace amin, raihana ta miƙe zata zata fita shima baba ya miƙe ya biyo bayanta, yana cewa mamana ki fito da miji kiyi aura kinji ko?"" to kawai tace tayi gaba, shima fita yayi daga gidan dan tafi wurin aiki......

������
*zawarci*
������

Raihana tana fitiwa ɗakinsu ta shiga ta fiddo wankin da zata yi, ta fara wankinta, *zawarci*
[21:18, 08/11/2017] ‪+234 813 308 2423‬: ����������
��������
������
����
*ZAWARCI*
����������
��������
������
����

*page* 7⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ��✍��

*JAMEELA MUSA*

����������
��������
������
����
�� *ZAWARCI*

Wannan shafinki naku ne, *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION*

Godiya ta musamman, *ASMEENAT XEEYAN* ��

*Y*ana fita tafi bayanshi da harara tace banza sakarai,,, kwanciya tayi tare da jawo bargo ta lulluɓe, taci gaba da baccin ta,,,,,

*A*minu kuma yana zuwa ɗakinshi gado ya hau ya kwanta, ya fara tunanin wata ƙawar *raihana* da take masifar sanshi, ajiyar zuciya sannan yace Allah sarki itama haka take ji, yanda yake ji idan raihana ta wulaƙanta shi, gyara kwanciyar shi yayi sannan yace ita kuma babu ruwanta bata jin komai, a bayyane yace Allah sarki rayuwa,,,,,,

****** ƙarfe 9:30am ta farka daga bacci, saboda haka a hanzarce ta miƙe ta shiga toilet tayi wanka, bayan ta gama wanka ta fito, ta zauna a gaban madubi ta fara shirya kanta,,,,,,,,,****×

*A*minu yana ɗakinshi yaji ƙamshin turaren raihana, shima tashi yayi ya shiga wanka, bayan ya fito ya shirya cikin ƙananan kaya, sannan ya nufo ɗakin raihana, itama ta gama shiryawa, ta matse cikin riga da wando, yana shigowa ɗakin a siƙwane ya isa inda take, ta rungumota , ta baya, ya ɗora fuskarshi saman kafaɗarta, daidai saitin kunnenta yayi magana, kinyi kyau madam, cikin masifa ta ƙwace jikinta,, ta juyo ta nuna shi da yatsan ta,, sannan tace wallahi daga yau sai yau, idan ka kuskura ka sake tiƙeni , ban yafe maka ba, dariya aminu yayi sannan ya sake matsawa kusa da ita, ya ƙara tallafo ƙugunta, ya ɗora hannuwanshi a saman ƙirjinta, raihana tace Allah ya isa ka taɓa, dariya ya sake yi sannan yasa hannunshi cikin rigarta, da sauri ta ciro hannu sannan ta ɗunƙule hannunta da niyyar kai mashi nushi yayi sauri yaja da baya,,,,,,,,,,

*H*aba madam ya kamata ki kawo man ɗan abinda zanyi break mana,,, raihana tace kaji wani sakarci kuma, madam sai kace wata inyamura`?"" Aminu yacd wallahi ba inyamura kike ba,,,, raihana taci gaba da cewa wallahi har inbar gidan nan bana girki kaji na faɗa maka, dan daga yau ka fara lissafi sati ukku zanyi gidanka, aminu yace Allah ya sawake, ni bana sakin mace duk abinda tayi man, raihana tace baka haɗu da irin raihana ba, dan wani abun idan nayi maka kai da kanka zaka rubuta saki ka bani, kuma idan kazo bani saika duƙa,,, aminu yace to Allah kada ya nuna mana ranar,,,, taɓe baki tayi sannan tace ka kawo man abinda zanyi kalaci, yace bara in dafa maki, ko inda yake bata kalla ba, shi kuma bai sake magana ba ya fita yabar ɗakin"""""""

*A* kicin haka ya zuge yaci gaba da aikin haɗa masu abinda zasuyi kalaci,,, ya daɗe sannan ya gama ya fito, da abinda yayi a farlo yaje ya ajiye,, ya koma kicin ya gyara inda ya ɓata,,, bayan ya gama ya dawo farlo ya zace ranki ya daɗe fito an gama, raihana ta taho cikin isa da ƙasaita, tazo ta zauna, yawo flaks tayi ta fara haɗa kalaci, sannan ta jawo flet na dankali da doya, ta ajiye a gabanta ta fara ci, aminu yabi ta da kallo, saida ta gama shi har lokacin babu abinda yaci ko yasha,,,

***miƙewa tayi zata nufi ɗaki da sauri ya miƙe ya riƙota,,,, farlo ya dawo da ita ya zauna saman kujera, ita kuma ya zaunar da ita saman cinyarshi, raihana kiji tsoron Allah, kada ki manta sadaki na bayar na auroki dan ina sanki, kuma na ɗauki hutu a wurin aiki na dan kawai in more da amaryata, a daidai lokacin da yake kai bakinshi cikin nata, raihana ta fara tureshi , amma a banza, haka taci gaba da halbe halbenta, tana tunkuɗeshi amma ko motsi baiyi ba, haka yaci gaba da bi duk inda jijiyar jikinta take yaci gaba da aika mata saƙonni, a kasalance raihana ta samu ta janye bakinta daga nashi, cikin wani yanyi tayi magana tace ban yafe maka ba, a hankali ya sake mata hannu , ya kwantar da bayanshi jikin kujera, ita kuma tana zaune a ƙasa,,, daga baya kuma ta miƙe ta nufi ɗakinta,,,, tana zuwa gado ta hau tayi ruf da ciki, zuciyarta tana mata saƙe saƙe,,,,,,

Shi kuma har lokacin yana zaune kamar yanda raihana tabarshi,,,,,,,,,,

Kiran sallar la"asar ne yasa umma cewa tashi muyi sallah mu dawo, *raihana* tace to, raihana ce ta fara fita daga ɗakin, umma har yanxun tana zaune inda take, raihana tana fita, umma tace to ai ga *zawarci* Allah ya ɗora maki raihana da ƙananan shekaru saidai addu"ar Allah ya kawo miji na gari,,,miƙewa tsaye tayi itama ta fito, a daidai lokacin da raihana zata shiga ɗaki,,, ta shige umma ta fito,,,,,,

������
*zawarci*
������
*R*aihana, ki fito fa babu ruwa a gidan nan, gwaggo ce take magana, raihana da take zaune saman abin sallah , tace *innalillahi wa"inna ilaihir raji"un* a daidai lokacin da gwagho ta sake cewa in banda iskanci ina magana sai kiyiman shiru , to ai sai ki fito ki faɗa man idan ni kike so inje in samo ruwan nan, miƙewa tsaye raihana tayi ta fito tsakar gida, ta fara tattara kayan mutane data wanke, gwaggo tace a nan zaki samo man ruwan, wani bokiti ta ajiye a gaban raihana, amma har yanxun raihana batayi magana ba, ta gama ƙwashe kayan ta nufi ɗakin su,

*zawarci*
*B*ayanta gwaggo tabi tana cewa uwarki kika kyale, shegiya mai baƙin halin tsiya, saboda wannan baƙin halin yasa namiji ya sakoki gaki nan kin rasa mashin shini, ita dai raihana batayi magana ba, saboda haka tana ajiye kayan ta ɗauki hijabinta tayi waje,,,,,,,

������
*zawarci*
������
*A* kofar gida ta tsaya har ta samu mai ruwa, tace ya kawo mata jarka ɗaya, yace to, ya ɗauko ruwan tayi gaba yabi bayanta,, har cikin gida, inda gwaggo ta ajiye bakitin ta nuna mashi a ciki ya fara zuba ruwan, gwaggo tana ɗaki taji ƙarar zuba ruwa saboda haka tayo waje, salati ta fara tana tafa hannunwanta yanxun saboda tsabar bakin ciki kije ki samo ruwan shine ke mai arziki zakije ki karawo mai ruwa?""" wannan ai baƙin ciki ne, naira ishirin ɗin idan kika bani ai na siyi omo, raihana ba tayi magana ba, mai ruwa yana gama zuba ta bashi kuɗin shi , ya fita daga gidan ita kuma ta nufi ɗakin su, gwaggo tace kai yarinyar nan Allah yayi maki baƙin ciki , raihana Allah ya tsine maki albarka tunda kika hanani kuɗin nan, raihana da sauri ta fito daga ɗaki sannan tace , baƙin bakin ki ya faɗa kanki dake da "ya"yanki da jikokinki , sannan ta koma cikin ɗaki, gwaggo tayi ta zage zage ita ɗaya a saƙar gida,

*zawarci*
Saboda dama tun dawowar raihana gwaggo bata da yaron aike sai ita, tun tana cewa bata zuwa, ta haɗata da baba yace tayi haƙuri taje saboda a zauna lafiya,,,

***gwaggo sai Allah ya isa take tana ƙarawa tana tsine ma raihana saboda bata bata naira ishirin ba, daga umma har raihana babu wanda ya sake ma gwaggo magana har ta gaji da kanta tayi shiru,,,,,,
[21:19, 08/11/2017] ‪+234 813 308 2423‬: ����������
��������
������
����
*ZAWARCI*
����������
��������
������
����

*page* 8⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ��✍��

*JAMEELA MUSA*

����������
��������
������
����
�� *ZAWARCI*

*H*aka gwaggo tayi jarabarta harta ƙoshi dan kanta,,,,,,

*Y*aro ne, tsaye a tsakar gida , sai ƙara nanatawa yake ance ana sallama da *raihana* gwaggo ce ta fito daga cikin ɗaki tana cewa uwar baƙin hali kinaji ana kiranki baza kixo ki fita ba,, to kada Allah yasa ki fito ni bara inje, idan ya shirya zance kawai ya turo, tana faɗin haka tayi waje,,,,
������
*zawarci*
������
*A* zaure gwaggo ta sameshi ya jingina da bango, ƙafarshi ta dama ya ɗorata a bango ta baya,, ya rungume hannunshi a ƙirjinshi, kanshi yana kallon ƙasa, kana ganinsa, sallama gwaggo tayi , ya masa ba tare daya kalli inda take ba, gaban gwaggo ya faɗi, da sauri ta leƙa kofar gida, dan taga ko mai sallamar yana waje, babu kowa dowowa tayi, kallon da tayi mashi yafi ƙarfin ace yaxo neman *raihana* saboda haka ta dawo, tace kaine ka aika yaro cikin gida?"" sai a lokacin ya ɗago kanshi , da sauri gwaggo ta sauke idon ta ƙasa saboda wani abu taji ya shigar mata cikin ido, zuuuuuuu, yace Eh , *raihana nake nema, gwaggo cikin rawar murya tace , lafiya dai?"" yace lafiya qalau ia san ganin ta ne, har yanxun kan gwaggo ƙasa yake, tace an ɗaura mata aura, ummm yace, ba tare da ya sake magana ba, hannunshi ya saka a aljihu ya ɗauko bandir na 1000, ya miƙa mata, gwaggo da sauri ta ƙarɓa, tana godiya shi kuma ya fita, da sauri gwaggo ta miƙe tayi cikin gida,,,,,,,,,,,

<<>> {{}}~~¤
*A* ɗaki gwaggo ta duba kuɗin sannan ta jinjina kanta, tace lallai ina da sauran aiki a gabana,, wannan mai kuɗin idan ya auri *raihana* ai ina cikin matsala, hijabinta ta jawo daga saman kyaure ta zura tayi gaba{{}}}<<>>

������
*zawarci*
������
*S*allamar baba tasa da umma da raihana suka fito tsakar gida, baba sai ƙara faɗaɗa murmushin shi yake,, tabarma umma ta shimfida tana ƙara mashi sannu da zuwa,, yawwa yake cewa lokacin daya ke zama, suma zama sukai baki ɗayansu, baba yace albshirin ku?"" da umma da raihana suka ce goro, sannan umma tace ai yau yanda naga kana murmushin nan, nasan an samu nasara, baba yace gaskiya alhamdulillah a daidai lokacin da gwaggo tayi sallama ta shigo, inda suke zaune ta nufa tare da ɗauko kujera tayani gulma ta zauna, baba yace to yaudai *raihana* Allah ya temakeki kin samu mijin aure, gaban raihana ya faɗi da sauri tasa hannunta ta dafe ƙirjinta,,, cikin zaƙuwa gwaggo tace sirikin namu daga ina yazo?""" baba yace ai ba ɓoyayye bane , *yusufa* mai niƙa ne,!'""""""" idanuwa raihana ta zaro sannan tace haba baba, ka daina wannan naganar don Allah mutum da mata ukku yara ashirin da wani abu, gwaggo tayi karaf tace rufa ma mutane baki munafikar Allah, ubanki yana magana kina magana?"" wannan ai rashin tarbiyya ne, sannan ta juya wurin baba tace a gaskiya idan kana biye ma yarinyar nan babu ranar da zata aure, tunda an samu mai santa kafin ya zare kawai kace ya turo, baba yace, ai yace zaizo su fahimci juna dai, saboda haka yaune zai fara zuwa, wata irin guɗa gwaggo tayi , sannan tace lallai yarinya kinyi goshi{{}}

*zawarci*
*U*mma batayi magana ba, ta tashi tayi ɗakinta, raihana ma ta rufa mata baya,,,, gwaggo ta zauna taci gaba zuga baba, lallai yace ma yusufa ya turo, kawai a ɗaura aure in yaso daga baya ta tare, haka dai taci gaba da maganganunta, daga baya ta tashi tayi ɗakinta, shima baba ɗakinshi ya shige,,,,,,,,,{{}}

{{}} gwaggo sai zagaye gida take tana cewa wallahi Allah ya rufa maki asiri, kinga kiyi aurenki, ki huta, kai wannan yarinya da sa"ar rayuwar kike,{{}} tanayi tana "yar dariyarta, kana ji kasan dan wulaƙanci take abun,, {{}}

{{}} *zawarci* {{}}
*R*aihana tace umma wallahi da baba baya nan dana fita nayi ma gwaggo magana, ince ta fita harkata, umma tace ki barta tayi duk abinda taga dama, abinda mutum yayi mai kyau ko kishiyar hakan kanshi yayi ma,,,,,,,


*U*mma tace tashi muyi sallar isha"i ki ida man labarin {{}}

������
*zawarci*
��������
*D*ariya *raihana* tayi sannan ta ɗauki buta, alwalla tayo ta dawo ɗaki hijibinta ta saka sannan ta haye saman abin sallah,,,,,,,,,,,

*AMEENCI WRITER'S ASSICITION* ��✍�� ke maku fatan alkairi, ni *jameela musa* nake cewa ku kasance tare dani, ��💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦💦
💦💦
*ZAWARCI*
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦💦
💦💦

*page* 9⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻

*MEELAT MUSA* 🌹

🔵🔵🔵🔵🔵
🔵🔵🔵🔵
🔵🔵🔵
🔵🔵
🔵 *ZAWARCI*


*R*aihana tana gama sallar isha"i, tana zaune a inda tayi sallar bata tashi ba, umma tace mata tunda kin gama ci gaba da bani labari, umma bata gama rufe bakinta ba, gwaggo ta yaye labulen ɗakin umma babu ko sallama tace, maza fito ga ango can mijin amarya yaxo, yana ƙofar gida yana jiran *raihana* farin cikin shi, ta ƙareshe maganar tana dariya,

*T*saki raihana tayi sannan tace bazanje ba, gwaggo tace ni kike faɗa ma haka?"" raihana tace an faɗa idan kinji haushi shima ki koreshi tunda dama kin saba ƙorama man samari,

Gwaggo tace wani in ƙori yusufa ace ina baƙin ciki?"" tana maganar tana taɓe baki, raihana tace ai dole yanxun kice haka tunda kinga shi ba aminu bane, gwaggo tace keji ɗiya yau kuma jarabar rashin auren naki a kaina zata ƙare?"""""

Rainaha tace dole ta ƙare a kanki tunda babu munafikar da ta kashe man aure sai ke, idanuwa gwaggo ta zaro sannan ta daki ƙirjinta da ƙarfi tace lallai yau naga sherrin rayuwa, raihana tace wallahi idanma har sharrin rayuwane baki ga komai ba, gwaggo tace to babu damuwa yanxun dai kije ga sabon miji yaxo, idan har kika yi auren banma kara zuwa gidan bare aja mani sharri,

Raihana tace zanje bisa cika umarni mahifina, tana faɗin haka ta miƙe tayi waje fuuuuuuuuu tunda dama hijabin da tayi salla bata cire ba, gwaggo tace shegiya mai baƙin hali ai gara dai a lallaɓa a aurar dake ga yusufa ko aikin gidan "ya"ya yasa ki ladafi, ɗiya tsaitsaye haka kamar an jika shinkafa da ruwan sanyi?"""" umma dai bata ce komai ba, haka gwaggo tayi ta wulaƙanci daga baya kuma ta nufi ɗakin ta,,,,,,,,


A ƙofar gida, raihana ta samu yusufa tsaye, yasha gayu fuskar nan ya nemi mai ya lafta mata sai ƙalli take, haƙoran nan nashi kuma dayaci goro suma sai yauƙi suke, haka raihana tabi yusufa da kallo tun daga tsakiyar kansa har ƙafafuwanshi,

Bayan ta gama kalleshi tsaf, ta dawo da duban ta daidai idon shi, suka kalli juna ido cikin ido, sannan tace sannu, ya yashe baki yace raihana raihana, tsaki raihana tayi sannan tace da Allah malam naji saƙonka, yanxun ka shirya auren *RAIHANA* ne?""""

Yusuf yace Eh darling, tsaki raihana tayi sannan tace to na baka daga yau zuwa jibi jibin nan, kaje ka haɗo man milayan biyar, idan har ka haɗo man su to lallai kaxo a ɗaura mana aure,

Idanuwa yusufa ya zaro sannan yace miliyan biyar fa kike magana?"""

Raihana tace Eh ba raihana kake so ba?""" yace Eh tace to madamar kana san aure na, sai ka kawo kuɗin nan idan kuwa ba haka ba, kada ka kuskura in sake ganin ƙafar ka a ƙofar gidan nan,

Ajiyar zuciya yayi zaiyi magana raihana ta ɗaga mashi hannu sannan tace ba wata magana tsakanin ni da kuma kai idan har ka kawo kuɗin to idan har baka kawo ba, bazan sake saurarenka ba, tana kaiwa nan tayi cikin gida..................

Yusufa yabi raihana da kallo har ta shige cikin gida, tana shiga ya ƙare ma gidan su raihana kallo yace lallai wannan yarinyar tama raina ma mutane hankali in banda iskanci ko ubanta bai taɓa ganin miliyan ɗaya ba amma shine har take cewa wani ya kawo mata miliyan biyar, tsaki yayi sannan yace zanga uban naki in faɗa mashi tunda shi mutumin kirki ne, haka yayi ta surutanshi shi ɗaya daga baya kuma ya tafi yabar ƙofar gidan.................

Raihana tana dawowa gida, ɗakin ummarta tayi sallama ta shiga, umma dake kwance har bacci ya fara fizgarta, tace har in dawo?""" raihana tace Eh, umma tace baima wani daɗe ba, raihana tace Eh, umma tace to ya kukayi dashi, murmushi raihana tayi sannan tace umma gaskiya nace mashi kawai ya turo, ta ƙarasa maganar tana taɓe baki, umma tace to Allah yasa hakan shine alkairi, murmushi raihana tayi sannan tace alkairin ma ne, umma tace to bara inje in sanar da babanku, raihana tace tou, tashi umma tayi ta fita daga ɗakin, tana fita raihana ta kece da dariya, sannan tace duk dani ake magana, idan har bazan koma gidan Aminu ba, haƙiƙa dai in su namiji mai tsafta in aura amma na auri yusufa haka ai ko dariyar ƙawaye ta hanani sakat, gyara ƙafafunta tayi sannan ta kwanta, da hannunta ta lalabu ta jawo wani tsohon zani ta lulluɓe, bata daɗe da kwanciya ba bacci yayi gaba da ita...............


Umma bayan taje ɗakin baba ta faɗa mashi cewa raihana tace ma yusufa ya turo, baba yace to Alhamdulillah lamari yayi daɗi Allah ya tabbatar da alkairi, umma tace ameen, itama umma ɗakinta ta tashi ta nufo ta kwanta,



💦💦💦
*Zawarci*
💦💦💦

*T*unda safe raihana tana gama sallah gwaggo ta fito wai lallai yau gidan nan fa babu ruwa, saboda haka raihana ta fito ta tafi wurin mono ta samo masu ruwa, raihana dake kwance, saboda ta gama sallah ta kwanta ta huta gabanta ya faɗi,

Gwaggo ta iso ƙofar ɗakin tace ki fito ki samo mana ruwa nace gidan babu ruwa, raihana daga kwance tace bazanje ba, *innalillahi wa"inna ilaihir raji"un,* raihana saboda rashin mutunci ni kike zagi?"" kuma uwarki tana ji kina zagi na, har cewa take ki ƙara man, daga raihana har umma idanuwa suka zaro suna kallon gwaggo, taci gaba cewa saboda kawai nace ki ɗibo ruwa sai kawai kiyi ta zunguwara iyaye na zagi,

Wayyo Allah da mutunci na gidan nan tunda ɗiyar nan ta dawo take ɗura ma iyayena zagi, lallai yau basai gobe ba, zamana gidan nan ya ƙare, baba dake ɗaki ya fito yana tambayar ba"asi?"""

Kuka gwaggo take sosai tace raihana ce tun shekaran jira da tayi magana sai ta zageta kuma uwar tana ji saidai tayi dariya,

Baba yace ina raihanar take?"" umma ta fito daga ɗaki tace wallahi ba haka akayi ba, yace rufe man baki, umma tayi shiru baba ya kalli inda raihana take tsaye yace daga yau shine magana na ƙarshe nasha faɗa maki idan baki kiyaye ba, haƙiƙa zaki bar man gida kinji na faɗa maki, raihana tace tou baba insha Allah amma wallahi ban zage ta ba, baba yace koma dai miye keta shafa bani ba, maza kije ki ɗauka ki ibo mata ruwan, da kina gidanki zataje can ta kirawo ki?""" raihana tace tou, ɗaki ta koma ta ɗauko hijabinta, kofar ɗakinsu ta ɗauki bokitin ƙarfe, ta ɗauka tayi waje...............................

Raihana bayan ta fita, baba yace ma gwaggo kema banda masifa tunda safe sai kice yarinya saita ibi maki ruwa?""" gwaggo tace ai tuwo zan ɗora dan anjima gidan biki zani, baba yace to miyasa tun jiya ba"a samo ruwan ba?"" gwaggo tace saboda sirikina zai zo, kuma almajira ma idan ka kira basu zuwa, tsaki baba yayi sannan ya nufi ɗakin shi itama umma ɗakinta ta koma gwaggo kuma tabi baba ɗakin shi ta fara tattaro kayan shi da sukai datti........................




A madadin *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ni *MEELAT MUSA* nake cewa ku biyoni ..........................................
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦💦
💦💦
*ZAWARCI*
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦💦
💦💦

*Page* 1⃣0⃣

*AMEENCHI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻

*MEELAT MUSA* 🌹

🔵🔵🔵🔵🔵
🔵🔵🔵🔵
🔵🔵🔵
🔵🔵
🔵 *ZAWARCI*

*T*saye take a bakin mono ta jera layi da bokatin ta, ga ɗan sanyi sanyin asuba, Raihana ta buɗe idanuwanta duk wurin babu mace sai maza, baƙin ciki ko miye raihana ta tuna oho?"" kawai hawaye ya fara gangarowa daga cikin idanuwanta, haka taci gaba da kuka tana gogewa da gefen hijabinta,

Kuka take tana matsawa da layinta idan an janye, haka kowa yaci gaba da ibar ruwa har layi yazo kanta, haka ta matsa ta tara nata, ta koma ta fara bugawa, har bokatin ya cika, tazo ta janye ta ɗauka ta nufo gida tana mai nadamar wannan *zawarci*

Sallama raihana tayi ta shiga cikin gida, a ƙofar ɗakin gwaggo taje ta ajiye ruwan, har zata juya gwaggo tace yawwa ga kayan babanki nan sunyi datti sai ki siyo sabulu da ruwa ki wanke, raihana tace sabulu da ruwa kuma?"" to a ina zan samu kuɗin siye?"""

Ggaggo tace cikin kuɗin da kikai wanki jiya?""" murmushi raihana tayi sannna tace to Alhamdulillah Allah ya ƙara rufa mana asiri, gwaggo tace Allah ya tona maki asiri raihana muje abinda kike boyewa, raihana tace innalillahi wa"inna ilaihir raji"un Allah dai ya tona maki asiri gwaggo ni kuma nawa ubangiji ya rufe man shi,

Gwaggo tace lallai raihana iskancinki kullum gaba yake, yanxun nan ubanki yayi man tsakani dake amma shine dai baza ki fita hanyata ba?"""

Raihana tace nima idan har baza ki fita tawa ba banga abinda zai fitar dani taki ba saidai a raba gidan nan, dani da ummana daban ke kuma dake da baƙin halinki,


Wannan magana tayi ma gwaggo ciwo saboda haka ruwan da raihana ta ibo ta ɗauko bokatin ta kwarara mata su duka a jikinsu, sannan ta ɗaga bokitin taci gaba da kwaɗa ma raihana,

Raihana sai kuka take tana faɗin a taimaketa gwaggo zata kasheta, baba da bacci ya fara ɗauka da sauri ya fito tsakar gida, amma umma duk abinda ya faru tana ji , amma bata ce ta tafasa bare a shiɗe, kuma haka bata fito tsakar gidan ba,

Baba yazo ya riƙe bokitin sannan yace ma gwaggo wai wannan wane irin masifa ne?""" gwaggo cikin shashsheka ta alamar gajiya kamar wanda tayi gudu sosai, tace tun da safe ɗiyar nan take zungurawa sale mai kanwa zagi, baban gwaggo kenan, taci gaba da cewa kuma idan mutum yayi magana a bashi rashin gaskiya,,,,,

Inda raihana take tsaye tana kuka baba ya kalla wanda duk gwaggo ta farfashe mata kai, baba yace ke kuma baki zaunuwa wallahi, baba na faɗin haka raihana bata sake bi ta kanshi ba tayi ɗakin umma,

Baba yabi ta da kallo, ita kuma tana shiga ɗakin ta fashe da kuka tace umma saboda Allah ni babu mai goya man baya?"" baba kullum bayan matarshi yake bi, umma tace kema da a gidanki kike ai mijinki zaibi bayanki ne, raihana tace Allah yaman sakayya umma dai batace komai ba, ita kuma raihana zama tayi sai Allah ya isa take yi,

Daga baya umma ta fita daga ɗakin, ita kuma raihana zama tayi taci kukanta ta ƙoshi, saida ta gaji dan kanta sannan ta tashi ta cire kayan jikinta, ta kwanta wani wahalallan bacci yayyi gaba da ita,,,,,,,,,,,


*zawarci*

Ƙarfe 12:30pm raihana ta farka daga bacci, fitowa tayi tsakar gida, a ƙofar ɗakin umma taga wani tashin wanki, an kawo mata, inda gwagg take ta kalla, ita kuma gwaggo surfe take k uwarmi take surfawa oho?""""

Kanta ta dafe da yake mata wata irin sara, dafe kan tayi sannan ta duƙa ta ɗauki buta ta nufi bayi, { *toilet* } tana fitowa ta nufi inda suke sanwa ta fara bubbuɗe kwanuka, gwaggo uwar mi kike nema?"" ko inda take raihana bata kalla ba, taci gaba da buɗe buɗenta, dariya gwaggo tayi ta dakata da dakan da takeyi, ta ɗora guwar hannunta kan taɓaryar dake cikin turmi, sannan ta tallafe fuskarta da tafin hannun ta, tace yarinya babu abinci, sai kinsan matsayi na a gidan nan sannan zaki fara cin abinci, murmushi raihana tayi sannan tace aikin banza kare da gudun layya, tana kaiwa nan tayi ɗakin umma, gwaggo tace saida a mutu da yunwa""" raihana dai bata sake magana ba, ta koma ɗaki madubi ta ɗauko tana kallon yanda gwaggo taci ma fuskarta mutunci,

Allah yayi man sakayya haka rainaha kawai ta faɗa , ta koma ta kwanta, wani bacci wahalar ya ƙarayin gaba da ita,,,,,,,,,,


💦💦💦
*zawarci*
💦💦💦

*R*aihana tashi kiyi sallah mana, umma ce take tashin raihana , a gajiye raihana ta fara buɗe idanuwanta da sukai mata nauhi, hawayen wahala suka fara safa da marwa a idonta, umma tace ki tashi kiyi sallah nace, a daidai lokacin da umma take cire hijabin jikinta,

A gajiye raihana ta miƙe ta fito, buta ta duƙa ƙofae ɗakinsu ta ɗauka, gwaggo sai habaici take, tsaki raihana tayi sannan tace idan dai kare yana haushi idan bai samu aboki ba ya zama mahaukaci, gwaggo tace uwarki waccan tana nuna ɗakin su to itace mahaukaci, kuma itace karya, dariya raihana tayi sannan tace ga irin halin nan kinayi , gwaggo tace shegiya mai baƙin hali, raihana tace ai a turbar kika ɗrani tun ina yarinya,

Gwaggo tace zawarar banza, raihna tace , Allah ya kaddara man kuma kema dake da ahalinki Allah ya ɗora maku jawarci kuji abin idan daɗi ne,

Gwaggo tace ni kike cewa "ya"yan na zasui *zawarci*? Tsaki raihana tayi , bata sake magana ba ta fara alwalla,

Gwaggo sai masifa take, ala dole wai raihana tace za"a sako mata "ya"ya daga gidan aure, taci gaba d cewa ke kaɗai kika zamo haka kuma kece kaɗai zaki lalace haka , a daidai lokacin da raihana ta gama alwalla tace tare dai zamu lalace mai faɗa da ɗiyar cikin ta, ki kashe mata aure dan ki aura ma ɗiyar aminiyarki, sai Allah ya maki abinda baki zato, tana faɗin haka ta shige ɗakin su,


Gwaggo kuma taci gaba da cewa anje an kashe aure uban waye yasa tun farko baki san mijin,?"" kuma har ki mutu baza ki samu wanda yakai darajar aminu ba, yar banza lalata,

Raihana dai bata sake magana ba, gwaggo ko banda tsinuwa da la"ana babu abinda take yi,,,,,,,,


Bayan raihana ta gama sallah , uma tace mata ga abinci can badiyya ta aiko maki dashi, kuma tace zata kawo maki wanki idan Allah ya kaimu, raihana tace tou, ɗauko abinci tayi ta matsa kusa da uma tace suci, ua tace ta ƙoshi, haka raihana ta caka hannu ta fara cin abincin,

Tana cin abinci umma tace raihana, kada ki kuskura ki sake cewa gwaggo ta kashe maki aure, abincin data ibo zata kai bakinta ta fasa kaiwa, tace umma wallahi itace ta kashe man aure, umma tace haka Allah ya ƙaddara kada ki kuskura ki sake faɗin haka kinji na faɗa maki ko?"" raihana tace Eh, umma tace gama cin abinci yau ki ƙarasa man labarin nan, murmushi raihana tayi tace to,


Haka tayi ta cin abincin bayan ta gama, ta fita ta wanko hannunta ta dawo, maganin da umma ta siyo mata ta miƙa mata, bayan tasha maganin ne, tace umma zan fara murmushi raihana tayi sannan taci gaba da cewa...........................




*MEELAT MUSA* ke cewa ku kasance tare dani!!!
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦💦
💦💦
*ZAWARCI*
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦💦
💦💦

*Page* 1⃣1⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻

*MEELAT MUSA* 🌹

🔵🔵🔵🔵🔵
🔵🔵🔵🔵
🔵🔵🔵
🔵🔵
🔵 *ZAWARCI*

*H*ar yanxun yana zaune inda raihana ta barshi a farlo , ya ɗan zame saman kujera ya kwanta, lallai wannan wane irin fitina ne?"" yana da mata amma shida babu uwarsu ɗaya ubansu ɗaya, tsaki yayi ya miƙe ya nufi ɗakin shi,

Yana zuwa babu ɓata lokaci wanka yayi ya shirya ya fito fess abunshi , ɗakin raihana ya dawo, bayan ya shiga ya sameta kwance saman gado, shima saman gadon ya hau, da sauri ta matsa da baya, hannunshi yasa ya jawo ƙafarta zuuuu ya matso da ita kusa dashi,

Saman ruwan cikinta ya hau, ya matsar da fuskarshi kusa da tata, daidai bakinta ya ɗora nashi, idanuwanshi suna kallon nata, sannan yace wallahi kiji tsoron Allah idan har kika kuskura a wannan halin kika mutu zaki haɗu da fushin Allah nine mijinki so da kauna yasa na aureki ki baki sona raihana ya kamata wani abun ki riƙa ragewa saboda rayuwa,

Wai miyasa ma baki sona?""" shiru raihana tayi saboda bata da dalili, riƙo haɓarta yayi da hannu, ya haɗa bakinshi da nata, da sauri ta fizge bakinta ta jawo wani kallabi ta goge bakinta , dariya yayi yace kyamata kike?""" raihana tace bana kyamarka nidai kawai bakai man ba,

Yace miyasa ban maki ba?""" a daidai lokacin da ya sauka daga saman jikin ta, raihana tace nifa ban taɓa ganinka ba, duka sau nawa na ganka aka ɗaura mana aure dakai?""" Aminu yace to miye aibuna?"" raihana?"" ya ƙarashe maganar yana kwantar da kanshi yayi yanayin tausayi,

Yace kiji tsoron Allah , ubangiji yana fushi da matar da take ma mijinta irin abinda kike man, ki daina abinda kike tun kafin ki haɗu da fushin Allah,

So nawa aka aurar da mace ga namijin da bata taɓa gani ba?"" kuma suna zamansu hankalinsu kwance, kiyi haƙuri ki soni kinji raihan?""" wallahi zan jiyar dake farin ciki?"" ya ƙareshe maganar hawaye yana bin fuskarshi,

Ajiyar zuciya raihana tayi sannan tace to kayi haƙuri duk abinda nayi maka insha Allah bazan sake ba, yace yawwa ko kefa?""" haka yayi ta mata nasiha, raihana tanajin nasiha tana bin jikin ta, amma fa har yanxun baiwai dan tana san Aminu ba, kawai saboda yana faɗi nata nau"in azabobin da Allah zaiyi ma wanda bata biyayyar aure yasa jikin ta yayi sanyi,,,,,,,

*** *** *** ***

*B*ayan haka da sati biyu, wata rana gwaggo ta kawo ma raihana ziyara da ita da aminiyarta *Ladi* raihana tayi farin ciki da zuwansu sosai sabida haka taje ta kawo madu ɗan abun ci da sha, bayan sunci sunsha, gawaggo tace raihana niko na ganki duk kinyi baƙiƙirin kin rame,

Murmushi raihana tayi sannan tace babu wani abu da nayi gwaggo, kawai dai dan kin daina gani na kike ganin haka, ta ƙarasa maganar tana taɓe baki, gwaggo tace to ya zaman naku yake?""" raihana tace *alhamdulillah* gwaggo tace amma gaskiya yaron nan yana cutar dake, raihana tace babu wani cutuwa muna zaune lafiya,

Gwaggo tace ai kece kike zaune lafiya dashi shi kwata kwata baya kaunarki, cewa yake daya samu yayi maki ciki zai sakeki ya auro wata, tunda dama baki sanshi, raihana ta ɗago ta kalli gwaggo cikin zaro idanuwa, raihana tace a,a, gwaggo Aminu bazai man haka ba, gwaggo tace baza ki gane ba, aike yarinya ce, tashi muje ladi, har yanxun akwai kuruciya a kanta,

Raihana tana ganin gwaggo ta mike tace gwaggo tsaya, gwaggo tace ai ina faɗa maki gaskiya bakya gani ne, raihana tace ni wallahi yana so na, kuma har kuka yake saboda yanda yake kauna na, gwaggo tace yaudara ce, ba sanki yake ba, raihana tace tou Allah dai ya sawaƙe, gwaggo tace amin, haka suka rantafa ita da ladi suka bar gidan...............

Fitar gwaggo da larai basu zame ko ina ba, sai gidan uwar mijin raihana, bayan sun gaisa gwaggo tace kin gane ni?""" maman Aminu tace na ganeki mana, gwaggo tace dama maganar yarinyar nan ne, dama maman Aminu bata san raihana, tunda taji labarin bata kaunar Aminu taji kuma tace itace ajalinsa, wannan dalilin yasa ta tsani raihana,,

Gwaggo tace dama cewa nayi tunda dai har yanxun naga ta kasa haƙura su zauna lafiya ɗiyar ƙawata na kawo dama ki haɗasu suyi aure, ita dama tana kaunar Aminu , tana sanshi tun tuni, maman Aminu tace to ai dama ya kwana da sannin bana kaunar yarinyar nan dole ya rabu da ita tunda ba tare aka haifesu ba,

Haka gwaggo taci gaba da zuga maman Aminu, daga baya suka tashi suka tafi daga gidan,

Suna fitowa gwaggo tace k sai in bari ta zauna a gidan can?"" duk tafi su bushira gidan miji, wato ɗiyarta kenan, da sauran "yan uwanta, tace shegiya sai ta fito wallahi, kuma babu ita babu ƙara auren mai kufi saidai ta samu talaka ta aura, haka sukaci gaba da magana suna kulla makircin su, daga baya suka rantafa suka nufi gida.................................,


Raihana zaune a gaban Aminu,

No comments:
Write blogger