spon

Sunday, September 2, 2018

Home Ba na tsoron fafatawa a zabe na gaskiya — Buhari

Subscribe Our Channel


HOME/POST FILE UNDER LABARAI
AUTHOR:AREWAINFINIT
DATE:SUN SEP 2 2018
 

NIGERIA PRESIDENCY
Image captionGwamnan jihar Lagos, wanda ake rade-radin cewa zai fice daga APC, na cikin tawagar Shugaba Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce ba ya tsoron fafatawa a zabe idan za a gudanar da shi cikin gaskiya.
Shugaba Buhari ya bayyana haka ne a yayin ganawa da 'yan Najeriya mazauna kasar China a birnin Beijing inda yake ziyara.
A cewar sa, "Ba na jin tsoron karawa a zaben da za a gudanar cikin gaskiya saboda shi ne ya sa na zama shugaban kasa. Na san irin faman da na yi inda sau uku ina tsayawa takara ina faduwa zabe amma ina kalubalantar sakamakon sa a kotun koli."
"Da na fadi a zabe karo na uku na ce 'Allah ya saka min'; daga bisani aka yi amfani da fasahar na'ura wuririn gudanar da zabe kuma hakan ya taimaka mana,' in ji Shugaba Buhari.

No comments:
Write blogger