spon

Monday, September 3, 2018

Home RA'AYI: NA SAN DAI BA ZA A HANA ALLAH YI WA BUHARI HISABI BA

Subscribe Our Channel


RA'AYI: NA SAN DAI BA ZA A HANA ALLAH YI WA BUHARI HISABI BA




RA'AYI:  Na San Dai Ba Za A Hana Allah Yi Wa Buhari Hisabi Ba

Daga Zee Taraba

Dan Allah masu yi wa Buhari makauniyar soyayya ida kun isa ku hana Allah ya yi masa hisabi ranar gobe tunda ku ba za ku fada masa gaskiya ba kuma ba za ku bari masu tsoron Allah su fada masa gaskiya ba.

Mun lura abun naku ya soma wuce gona da iri, har ta kai ga kuna zagin Malaman addini akan siyasar banza wadda kwata-kwata duk rantsi duk jimawa shekaru takwas kacal ake akan kujerar.

Mulkin Buhari babu hali Malami ya ce zai fito ya fadawa Buhari gaskiya sai a soma cewa wai malamin siyasa ne, idan kuma ya yaba Buhari sai a ce na addini ne tsabar son zuciya irin namu.

Wai shi Buhari yafi karfi a fada masa gaskiya ne?

A ce wai Malaman addini a ringa zagin su akan wani dan Siyasa wanda kullum shi a yabon kansa yake shi kadai tsabar son rai?

To bara ku ji na fada muku, idan kun hana a fada masa gaskiya a nan gidan duniya, to ku sani baku isa ku hana Allah ya yi masa hissabi ba bisa ga yadda ya gudanar da mulkinsa da kuma rayuwarsa ba ranar gobe.

Saboda haka a yi hattara dan Allah, Siyasa ba hauka bane.

No comments:
Write blogger