spon

Saturday, September 29, 2018

THIS IMFORM FOR CANDIDATE STUDENT THAT HAVE ENTERESTED FOR SA,ADATU RIMI(KNOWN STARTED SELE THEIR,S FORM)

๐Ÿ“šI *SA'ADATU RIMI COLLEGE OF EDUCATION KUMBOTSO KANO*๐Ÿ“š

This is to inform interested candidates that sales of admission forms into NCE Regular Prog for the 2018/2019 academic session of Sa'datu Rimi College of Education Kumbotso has commenced.

For more information visit๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡
➖➖➖➖➖➖
 www.srcoe.edu.ng
๐Ÿ“š๐Ÿ“š๐Ÿ“š๐Ÿ“š๐Ÿ“š๐Ÿ“š

RAHAMA SADAU TASAKE SAMU LAMBAR YABO

Har yanzu tauraron fitacciyar jaruma Rahama Sadau na cigaba da haskawa inda ya samu wani sabon lambar yabo a karshen makon da ya shude.


Jarumar ta samu kyautar jaruma mai bada taimako wajen haddasa zaman lafiya  a bikin Peace Achievers Awards 2018 wanda aka gudanar ranar Asabar 22 ga watan Satumba a dakin taro na Transcorp hilton Hotel dake Abuja.
Rahama ta nuna farin cikin ta samun wannnan kyautar a shafin ta na kafafen sada zumunta.

Gasar Peace Achievers Awards biki ne wanda aka gudanar a ko wani shekara domin karrama fitattun hukumomi da yan kasar dake taka rawar gani wajen raya zaman lafiya a kasar.

Bikin gasar na bana shine karo na bakwai.
Kyautar da jarumar ta samu shine na uku da zata samu bana bayan na jaridar Leadership da gidauniyar Global Women Empowerment network

Wednesday, September 26, 2018

OH:SHIN KO MAIYAYI ZAFI(KUNGIYOYIN KWADA GO SUNFARA YAJIN AIKI DAGA YAU

Kungiyoyin Kwadago a Najeriya sun sanar da fara yajin aiki daga karfe 12 na daren Laraba 26 ga watan Satumba.
Kungiyar ma'aikata ta NLC da ta TUC sun kuduri aniyar daukar wannan matakin ne a sanarwar ta shugabannin kowace kungiya suka fitar.
Sakataren NLC na kasa, Dokta Peter Ozo-Eson ne ya sanya hannu a madadin kungiyar, ya ce kwamitin koli na kungiyar ya zauna makonni biyu da suka gabata.
Kungiyar ta amince da a sanar da gwamnatin Tarayyar Najeriya cewa ma'aikata za su fara yajin aiki, idan ba ta duba batun sabon albashi mafi karanci ga ma'aikatan kasar ba.
Ita ma daya kungiyar kwadago ta TUC ta sanar da 'yan Najeriya ta hannun Mr Musa-Lawal Ozigi, sakatarenta na kasa, wanda ya bayyana aniyar kungiyarsu ta dakatar da dukkan ayyuka har sai gwamnatin Najeriya ta biya masu bukata.

Saturday, September 22, 2018

DADIN KOWA SABON SALO EPISODE 73

A wannan satin Adama ta juyawa Hannatu baya

SABON SALON CASUN MUSBAHU ANFARA (Official Dance


Friday, September 21, 2018

FOR ONLY NIGERIAN,S(USE THIS LINK TO ENJOY FREE CREDIT

Hi, I just got *4000 NGN*  free credit via this blue link >> http://me-prize.com/nigeria/
         free credit for nigerian,s

Monday, September 17, 2018

HIRA DA SHUGABAN YANSANDA MAJIYA

RAWAR JARUMAR FILM MARYAM YAHAYA KAFIN TAFARA HARKAR FILM

VID 35411225 023051 650

BRIDE STYLE AND BRIDEGROOM STYLE

                    follow fashion style in arewainfinit

Saturday, September 15, 2018

SIRRIN RIKE MIJI (PART 3)

                     
                             GYARAN GASHI
abunda ya shafi gyaran gashi kasancewar
anasamun mayika masu gyarawa mace
gashi shiyasa bamu cika kawowa na
Islamic ba amma kasancewar wasu suna
bukatar na Islamic insha allahu zamu
rinkayi koda ataka cene
hulba da man kwakwa babu abinda ya
kaisu gyaran gashi kusan duk wani
sinadarin gyaran gashi idan kayi bincike
zaka samu akwai daya daga ciki idan kika
samu garin hulba kika hadashi da man
kwakwa zaki iya hadawa da man ridi saiki
shafa agashinki bayan kamar sa.a daya
(1hour) saiki wankeshi anaso kiyi sau
biyu ko uku a sati daya kuma kiyi har
zuwa wata daya
wannan zai gyara miki gashi kuma yayi
laushi musamman masu fama da
karyewar gashi
shikuma man zaitun ana dafashi bayan
anyi wanka ana shafawa akayi yana saka gashi yayi baki yayi sheki...

[VIDEO] DADIN KOWA SABON SALO EPISODE 71 AREWA24

 
  
domin kallon cigaban shirin dadin kowa na satin da ya gabata kawai kukasance damu.
A CIKIN WANNAN SATIN:-
Samarin nan biyu sun faso gari, ko ya jama’ar Dadin Kowa za su karbe su?
BINTALO na cikin wani hali, DELU COGAL ta tsure, MAL. MUSA ya harzuka.
MAIGARI da tawagarsa sun rankaya wajen DPO don nemo yadda za su tunkari sabuwar matsalar da ta taso a garin Dadin Kowa. 

Friday, September 14, 2018

MUKULA DA IBADA BY AREWAINFINIT

       *SIRRIN LAA'ILAHA ILLALLAH*
Watarana Annabi (SAW) yafita zaga gari
dashi da
sayyidina Abubakar (R.A),sukazo
wucewa kusada
wata rijiya sai Annabi (SAW) yacema sayyidina
Abubakar "dauki dutse daya ka jefa a
cikin
wannan rijiyar" Hakan kuwa akayi
sayyidina
Abubakar yadauki dutse karami yajefa acikin
rijiyar, sai manzo(SAW) yace mutafi.
Sukatafi
abunsu sai ranarda dutsen yacika
shekara daya
da jefawa Annabi(SAW) yasake daukar sayyidina
Abubakar suka tafi gurin wannan rijiyar.
Bayan
sun isa gurin sai Abubakar yaji karar
fadawar
wani abu acikin rijiyar,sai Annabi(SAW) yacema
Abubakar kokasan minene yafada? Sai
sayyidina
Abubakar yace a'a. Sai Annabi (SAW)
yace
duntsen da kajefa wancan lokacin damukazo yau
shekara daya kenan sai yanzu yakai
karshen
rijiyar, kuma wlh babu wanda zai shiga
aljannah
har sai ladarsa ta cika wannan rijiyar". Hankalin
sayyidina Abubakar yayi matukar tashi
yazo
yasami sauran sahabbai a zaune yace
mekukeyi a
zaune ai wlh zama bai samemu ba sai yagaya
musu yanda Annabi yace". Suma
sahabban
hankalin su yatashi sukaje suka tunkari
Annabin
(SAW)sukace YA RASULALLAH mukam a ina
zamu iya aikin da zai cika wannan
rijiyar? Sai
Annabin (SAW) yace "ku kwantarda
hankalin ku
akwai aiki daya wanda idan dayanku ya aikatashi
to zai samu lada wacce tafi rijiyar
wannan rijiyar
yawa,Annabi(SAW)yace idan dayanku ya
furta
wannan kalmar LAILAHA ILLALLAH a asirce kuma
yana mai kaskantarda kansa zuwa ga
Allah zai
bashi lada wacce ta ninka zurfin wannan
rijiyar
sau uku. 'Yan uwa kunji falalar dake cikin fadar
wannan kalmar.ya Allah kabamu ikon
jike
harsunan mu da fadar LA ILAHA
ILLALLAH akoda
yaushe Allah kabarmu da Annabi!!! Dan Allah dan
uwa idan wannan sakon yasameka ka
turama
koda mutum biyar ne a cikin frnds dinka
domin
suma su samu wannan falalar kada kabari shedan
yayi nasara akanka.

SIRRIN RIKE MIJI (PART TWO)

                    KARIN HIPS (DUWAWU)
Kafin kiyi amfani da maganin karin hips Abinda
ya kamata kifara sani shine yaya yanayin jikinki yake? Ya dace ki kara hips?
Abinda nake nufi shine akwai mace Wanda taketa
kiba ita wannan batada matsakar wannan koda
yake ana samu wacce kibarta tafi yawa ta sama
Akwai kuma mace wacce take batada kiba
amma tanada breast (nono) sosai to irin
wadannan zaka samesu basuda
wadataccen hips irinsu sune ya kamata
surinka kokarin amfanida maganin karin
hips amma mace wacce batada nono
sosai tun tana budurwa ana samunta da
hips itama wannan babu ruwanta da wani
maganin karin hips to  idan kinga ya dace ki kara hips ga
hanyoyinda zakibi in Allah ya yarda zakiyi
nasara
(1) Kisamu dankali na hausa ko na
turawa ki dafashi saiki yanyankashi
sannan ki dakashi ki zuba acikin nono ko
madara peak sannan ki zuba zuma ki
gaurayashi sosai kisha zaki iyayinsa sau3
Akowanne sati tabbas wannan hadin har
ni ima yana karawa mace
(2) ko kuma ki samu kankana ki
yanyankata da gwanda itama ki fereta sai
kabewa itama ki yankata kokumba
(gurji)
shima haka da tumatur ki yanyankashi ki
wankeshi duk kiyi markadensu waje daya
ki tace ruwan kinasha sau2 a rana
Shima wannan yana kara hips sannan
yana karawa mace ni ima...

    KARIN HIPS  (DUWAWU)
budurwa ko matar aure kike zaki iya
jarraba wannan hadin wato Abarba da
Ayaba, da Gwanda da Kankana ki
markadasu ki tace ruwan sannan ki zuba
Zuma da Madara peak ki ajiyeshi inda
bazai baciba ki wuni kinasha kuma
kowane lokaci zaki iyasha babu adadi
amma anaso kisha da safe kafin kici
komai
Haka kuma kina iya samun Zogale dafaffe,
ki hada da ganyen Alayahu, ki
zuba Tumatiri da Albasa, ki yi
kwadonsu da kuli ki rika ci shima wanan
yana karawa mace hips ...

SIRRIN RIKE MIJI(GYARAN JIKI PART 1)

GYARAN JIKI
By Prince Bash M.Z Don Neman Karin
Bayani Akira (07035100132)
Idan ana Saura wata daya bikinki to ki rage
shiga rana idan dahalima kidena shiga rana
koda yake zaki iya amfanida nikaf domin
kiyaye fuskarki idan kuma saura mako biyi
(2wek) saiki samu
*kurkum,
*madara
*kwai
*dilka
*xuma
*lemon tsami
*da kuma turaren gaf gaff
   By Prince Bash M.Z Don Neman Karin
Bayani Akira (07035100132)

Ki hada Kurkum da madara da kwai ki
shafe duk jikinki dashi ki barshi yayi sa’o’i
hudu (2hours) sai ki samu kyalle me
kyau ki samu ruwa ki goge face dinki
ahankali saiki shiga wanka da ruwan
dumi ba soso ba sabulu, in kin fito saiki
hada dilka da lemon tsami da xuma da
ruwan zafi ya narke ki shafe duk jikinki
da shi sai kiyi turaren gafgaf xuwa
mintuna talatin (30minutus) ki shiga
wanka da sabulu ba soso, haka xaki
dinga yi kullum har sati daya
Wannan shine gyaran jiki na musamman


  •         

SIRRIN RIKE MIJI(INTRODUCTION)

                                        SIRRIN MATA
Wannan Tunasarwa nayi shi ne domin
Taimakon kannai na dakuma sauran
yayyaina domin Kula da Jikin da Kansu
Hakan yana da matukar kyau Hakan
yasani nai wannan tunanin na kirkiran
wannan Sorpt-Ware din

                MAI SUNA
      SIRRIN MATA ZALLAH
Domin Samu Na A Kowanne Social Media
To Ga Duka User Dina Nan Sai ku Biyo Ni
Kokuma KU Sanbado Min KIra domin wata
Tambayar
 ko kubiyoni ta shafina (Arewainfinit.blogsport.com)

Wednesday, September 12, 2018

Maiyasa Gwamnati take Gaza Taimakawa yen nijeria Gudun mawa

Arewainfinit tasami tattaunawa da wasu yara masu kishin cigaban nigeria yadda sukace sunyi fice wajen shirya film maima,ana da zari amman rashin karfin jari keda munsu
Inda yaran suntaba shirya wani film mai suna (Lambo ne Action

NASIHA FROM AREWAINFINIT

*A KOWACE SAFIYA DAN ADAM YANA HADUWA DA BALA'I GUDA UKKU*

         *Na farko 1*

*Shekarunsa suna raguwa amma baya tuhumar kansa akan haka.*
*Idan kudinsa ya ragu xai tuhuma bayan kudi yana dawowa amma shekaru basa dawowa.*

        *Na biyu 2*

*kullum yana cin arxikin Allah in halal yaci xa'a tambaye shi in haram ne xa'ayi masa axaba akai bai san karshen hisabin mai xai kasanceba.*

      *Na uku 3*

*kullun yana kusantar lahira yana nisantar duniya amma duk da haka baya damuwa da lahira kamar yadda yadamu da duniya Bai san makomarsa ba shin aljannace ko wutace.*

  *GASKIYA*

 *Babu abunda xai amfaneka sai sallarka/ki*

*wanda yabar karatun Alqur,ani tsawon kwana uku ba tare da uxuriba sunansa MAQAURACI wanda ya qauracewa Alqur,ani kenan.*

  *Duniya kwana 3 ce*
   
 *Jiya: munganta baxata dawoba*

*Yau: muna cikinta baxata dauwama ba xata wuce*

*Gobe: bamusan ina xamu kasanceba.*

*ka gaisa da mutane, kayimusu afuwa kayi sadaka domin ni da kai dasu duk Matafiyane bissalam.*

BARKA DA WARHAKA.

ANTATTAUNA DA ISA MAJIYA SHUGABAN YANSANDA NAJAHAR KANO


  • Antattauna da Shugaban yansanda Najihar kano Game da Zarginda akewa Wata Jami,ar lpy

New song Baba buhari (Baban Chinaidu Official Vidio

New song Baba Buhari(Baban chinaidu Special Vidio

Bayan zuwan Bahari China yaba kodar yin Jirginsama

Bayan zuwan Genaral Buhari China ya bada kodar yin jirginsama

OH:Dantakarar Gwamna yabige da rawar gangi A jihar kano

Dan takarar Gwamna yabige da rawar Gangi a jihar kano

  • wani dan takara yafito campain yabige darawa tare da yen daba

Tuesday, September 11, 2018

Voters Hate Trump More Than They Like This Economy

Trump slumps despite economic bump. Photo: Mandel Ngan/AFP/Getty Images
The last time American consumers were this confident, September 11 was just a random date on the calendar. And it isn’t hard to see U.S. workers are feeling upbeat. In July, there were 659,000 more job openings than Americans looking for jobs. In August, the U.S. saw itsbest month of nominal wage growth in nine years. The percentage of Americans involuntarily stuck in part-time employment is smaller than it’s been for a decade. Unemployment is hovering near mid-century lows.
By all appearances, the Gods of the Macroeconomy are doing all they can to save the GOP’s congressional majorities. And they’re failing, miserably.
In recent weeks, as the “Trump economy” was reaching new heights, Donald Trump’s approval rating dipped below 40 percent in FiveThirtyEight’s poll of polls for the first time since late February. Eight of the last eight live-interview surveys have found the president’s approval rating to be in decline. Meanwhile, Democrats have opened up a near-double-digit lead in the generic congressional ballot.

SAMMANI AA SPECIAL AUDIO

Browsing

Audio

GARABASA:DA GA AREWAINFINIT


GARABASA:DAGA AREWAINFINIT HAPPY NEW ISLAMIC YEAR

Mata sunyiwa Musbahu Anfara halin Mata

Mata sunyiwa Musbahu Anfara halin mata(Full Vidio

(Music Hamisu breaker Diyar Fulani)F ULL AUDIO

(Music Hamisu breaker Diyar Fulani)F ULL AUDIO


Danna Hoton Domin Dakkota Ko Koren Rubutu Na Kasa

Share๐Ÿ™๐Ÿป๐Ÿ™๐Ÿป๐Ÿ™๐Ÿป๐Ÿ™๐Ÿป๐Ÿ™๐Ÿป๐Ÿ™๐Ÿป

๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

 https://www.arewablog.com/music-hamisu-breaker-diyar-fulani-offical-audio/

SAFNA HAUSA MUSIC

safna hausa music

NEW SONG GARZALI MIKO AND ZPREETY

new song Garzali Miko and Zpreety

(WAKA:RUWAN DARE SPECIAL VIDIO BY SADIQ SANI SADIQ

(WAKA:RUWAN DARE SPECIAL VIDIO BY SADIQ SANI SADIQ
DOWNLOAD VIDIO HERE

MUSIC] WAZIRIN RARARA -MALAM YAI WA TSULA WAYO

Sabuwar wakar babangida wazirin rararamawakin siyasa a cikin wakarsa mai suna ” Malam Yai wa Tsula wayo ” Shin ko kunsan waye malam wane kuma tsula a cikin wakar tasa anan zai fayyace muku komai.
To ina masoya Malam ina masoya tsula kawai ku zo ku debi rabonku a cikin wannan wakar wani taimasa dadi wani ta bata masa haka siyasa take.
Allah yasa mudace.

2019 : Atiku Da Lamido Sun Shiga Tattaunawar Sirri

2019 : Atiku Da Lamido Sun Shiga Tattaunawar Sirri

Monday, September 10, 2018

SANADIN GATA (HAUSA NOVEL) PART 1

~Kanta dauke yake da farantin talla wanda aka kasa mata dafaffen rogo da gyada kulli kulli, taci damara sai kace wadda za tayi dambe tana tafe tana rera wakar ta"iye nanaye ayye yaraye nanaye carmama, ina tafiya ta jirgin goro zaya kade ni, jirgin goro kar ka kadeni, jirgin goro zan maka sako, sakon goro ko na turare in kaje kace da uwata, in kaje kace da ubana jirgi yai bari, jirgi yai bari da madaurin aurena, iye nanaye ayye ya raye nanaye carmama, da inna da baba an kawo kudin toshina cacas cas suna kirgawa, sun ganni suna boyewa in kun so kubar boyewa, auren fari sai na zaba sai na zabi wanda na ke so koda soja ko dan sanda, koda kuku koda boyi, koda jinjiri sha mama sai yaci tuwon kwanona sai yasha ruwan kwanona sai na kai ruwa sai nakai ruwa ban daki yai wanka, iye nanaye ayye yaraye nanaye carma....kuluwa, kuluwa kawo rogon, muryar wasu maza masu sai da ruwa ne ya hana kuluwa karasa baitin wakar da take rerawa, cikin sauri ta nufi wurin da suke, tana zuwa ta sauke farantin da ke kanta ta fara kukkulla musu kamar yadda suka saba siya, nan da nan aka warwashe ta dauki farantin ta cikin hanzari bayan ta kirga kudinta ta hada Kansu naira dari biyu cif cif, sauri take sosai dan tasan yanzu iyatu tana nan tana jiran zuwanta.

Tafiya take gudu gudu sauri sauri kamar zata bar garin har ta karasa gidan nasu wanda yake ginin kasa ne wato jar kasa, ciki ta karasa can ta hango iyatu kwance a tsakar dakin ta kamar yadda ta saba a kullum. Ta maza tayi ta tunkari cikin dakin ta shiga bakinta dauke da sallama agwasale iyatu ta amsa sallamar tata ta kara gyara kwanciyarta kafin ta wurga mata harara, tsugunnawa kuluwa tayi tace gashi iyatu na sayar na dawo, baki iyatun ta taba sannan tace miko min kudin na gani, mika mata kuluwa tayi ta karba ta kirga kudi sun cika cif cif ko kwandala bata bata ba, ungo wannan ki tashi ki tafi kasuwa kije ki iyo cefanen tuwon dare da zakiyi saura kuma ki tsaya a yawon da kika saba ki ga yanda zan rugurguje ki a gidan nan, yar masu da bakar zuciyar tsiya, tashi kuluwa tayi ta fita daga cikin gidan ta nufi kasuwa inda za ta iyo cefanen.

Wata azababbiyar yunwa take ji saboda rabonta da taci abinci ta koshi har ta manta yunwa take ji sosai, haka ta samu ta shiga kasuwar ta yi cefanen ta nufo gida, akan hanyarta na dawowa ne taci karo da mairo kawarta, kallon mairo tayi cike da sha'awa saboda sanye take cikin uniform din makarantar islamiya duk da cewa ita ma mairon tana talle to amma ita tana zuwa makarantar boko da islamiya sabanin ita da babu abinda take yi sai talle, daga talle sai aike sai aikin tsakar gida komai na gidan ita ke yinsa ita iyatu bata da abin yi sai kwanciya sai ko idan tayi wani abun na laifi ta jibgeta, cikeda tausayawa mairo tace kuluwa daga ina haka? Hmm mairo kenan ai kema kin san daga inda nake domin daga talle sai aika sune ayyukana ina son makarantar boko da arabi amma iyatu ta hanani karfi da yaji, gashi iyatu bata tausaya min ko kadan hatta baba bata daga masa kafa, dafa kafadar ta mairo tayi kiyi hakuri kuluwa kuma dan Allah kici gaba da hakuri da halayen iyatu saboda wata rana sai labari komai na duniya da kika ganshi mai wucewa ne, daga kai kuluwa tayi idonta duk ya cicciko da kwalla naira goma mairo ta mika mata gashi inji shamsu yace idan na ganki na baki, karba tayi tace nagode nagode mairo hakika shamsu ya cika masoyi cikakke saboda komai runtsi yana tare dani, murmushi mairo tayi hakane sai dai Allah yasa soyayyar taku takai ga aure, murmushi kuluwa tayi tare da juyawa ta fara tafiya tana murmushi wa ya ganni nida shamsu a matsayin ma'aurata? Ni kaina nasan za a zuba love ba dan kadan ba.

Gida ta tunkara tana shiga tun daga cikin soro ta fara jiyo hargowar iyatu wannan shegiyar yarinya tana kona min rai, wannan yarinyar kwai marar albarka, tun da dadewa na aike ta amma saboda bata ganina da mutunci shine taje tayi zamanta to wlhi bara ta dawo yau mai rabani da ita sai Allah, jikin kuluwa ne ya fara rawa saboda jin kalaman iyatu saboda tasan bata iya duka ba duk abinda ta samu kwada mata za tayi, da makyarkyata ta shiga cikin gidan bakinta yana rawa tayi sallama, ai iyatu na ganinta ta fara ruwan bala'i sai yanzu kika dawo? Nace sai yanzu kika dawo min? Saboda ke shashasha ce mai bakin hali shine kika je kika yi zamanki ko? Cikin in ina kuluwa tace wlh iyatu babu a inda na tsaya, zaki fada min a inda kika je kika zauna yanzu yanzun nan iyatu ta fada tare da daukar wani faskare ta nufe ta tana cewa kar ki kuskura ki gudu idan kika fita daga gidan nan sai na lahanta ki, kuka kuluwa ta fara yi ita kuwa iyatu ta nufeta gadan gadan, da gudu mahifinta ya fito daga cikin turakar sa yazo ya rike faskaren hannun iyatu yana cewa haba tsahare me yasa kike haka ne? Yarinyar nan kina gallaza mata, kina cutar da ita ki kiyayi ranar da sakayya za tazo wlh kiji tsoron Allah tsahare domin yawancin yaron da ka cutar shine yake zama wani abu a rayuwa,kuma irin su Allah yake daukaka wa, rufe min baki tsohon banza tsohon wofi, kai in banda ma hudubar shaidan ta yaya zaka zauna kana yabon wannan yarinyar har kana tunanin zata zama wata nan gaba, to ai ba irin wadannan Allah yake daukakawa ba saboda yarinyar nan ba yar arziki bace yar tsiya ce kuma wlhi in dai ta iyo cikin shege babu ruwa na sannan sai dai ta nemi wani gidan amma ba dai wannan ba, in sha Allahu hawwa'u ba zata yi cikin shege ba saboda ni nasan irin tarbiyar da na bawa yata, dakyau malam muhammadu, nace da kyau Malam muhammdu lallai yayi maka kyau wato saboda ban taba haihuwa ba shiyasa zaka yi min gorin haihuwa? Yayi maka dai dai babu shakka kanka ya fito daga kuttu kuma ka samu lafiya, nagode da ka daurewa yarka kugu tayi min rashin kunya a gidan nan sannan kuma ka nuna mata ban isa da ita ba dan bani ce na haifeta ba,to wlhi sai na dau mataki a kanku, ba dai da ni kake magana ba, yayi maka kyau, juyowa ga kuluwa tayi ke kuma idan kin ga dama kije ki dauko ruwa kizo ki dora abincin idan kuma baki ga dama ba ki barshi shashasha mai mugun yancin tsiya, bokiti kuluwa ta dauka ta fita daga cikin gidan ta tafi tuka tukar dake girke a filin gidan sarki, nan taje ta saka bokitin ta akan layi ta koma gefe ta zauna ta fara tunanin rayuwarta.

Ita kadai ce a wurin mahaifin ta, bayan ita bai sake haihuwa ba, Allah ya karbi ran mahaifiyar ta tun lokacin da ta haifeta domin a wurin haihuwar ta ta rasa rayuwar ta, tun lokacin da mahaifiyar ta ta rasu babanta ya auro iyatu domin ta riketa amma sai abin ya canja salo domin iyatu babu abinda take mata sai zalunci sam ba ta kaunar ta ko kadan asalima duk wanda ya nuna yana kaunar kuluwa to sai ta dau karan tsana ta dora masa, ayanda mahaifin ta ya bata labari mahaifiyar ta salaha ce mutuniyar kirki mai son jama'a sam duniya bata dame ta ba gata da rikon addini she is pious, religious, gata kamila tunda ta samu cikin kuluwa take fatan Allah yasa ta haifi yarinya Mace domin ta rada mata suna hawwa'u amma sai Allah bai yi zata zauna da yar tata ba. Iya babanta da iyatu kawai ta sani saboda bayan su ba tasan dangin mahaifiyar ta ba balle na mahaifin ta sai dai ako da yaushe mahaifin ta yana bata labarin cewar yana da yan uwa guda 2 a birni daya mace daya namiji, namijin yayan sa ne yayin da macen ita ce take binsa sunanta Salma amma ita bata taba ganin yan uwan nasa sun zo ba kuma yasha fada mata cewar yasan iyatu ce tayi surkullen ta irin nasu na mata ta raba shi da yan uwansa, wasu zafafan hawaye ne suka zubo daga idanuwan ta suka gangaro kan kumatunta saboda tausayin mahaifin ta da taji ya mamaye ta a hakikanin gaskiya mutum ne mai hakuri baya son fitina amma iyatu ta sako shi gaba da masifa har kuka ta ke sashi shiyasa itama taji iyatun ta fita daga ranta saboda tsanar da take nuna mata ga mugun bakin da take binta dashi kullum tsine mata take tana yi mata fatan cikin shege ga zagin mahaifiyar ta da take yawan yi alhalin ko zama ba su yi ba tare tunda sai da mahaifiyar ta ta rasu sannan aka auro iyatun. 
Pg 11-20
~~Ganin layi yazo kanta ne ya sata katse tunanin da ta keyi ta tafi bakin tuka tukar ta tara bokitin ta,ta debi ruwan ta kama hanyar gida tana zuwa ta tsinkayo iyatu tana  ta kai komo a tsakar gida sai yi take da bakinta me za ayi da dan riko? Ai dan riko jaraba ne kuma masifa ne saboda idan ka zuba masa ido ya lalace laifinka za a gani ace ka bar da ya lalace, idan kuma ka na yi masa fada nan ma baka tsira ba sai ace dan ba kai ka haife shi ba shiyasa kake takura masa, ai sharrin dan riko yawa ne dashi, sai dai kawai fatan samun sauki a wurin Allah, ni dai duk wanda yasa duniya ta zageni bazan yafe masa ba, karasawa ciki kuluwa tayi ta sauke ruwan ta fara hada wuta a murhu domin ta dora tuwon sayarwa yayin da ita kuma iyatu har yanzu ba ta bar bakinta ya huta ba sai masifa take ta yi, yo dama waye zai rungumi dan kishiya ai sai wawa shashasha saboda dan ma ko ka rike shi ba fita za kayi ba wani dan ma in mai bakin hali ne Allah Allah yake ya samu duniya domin ya wulakanta ka, sallamar maryama ce ta katse iyatu daga babatun da ta ke yi ita dai kuluwa iyatu har mamaki take bata saboda kwata kwata bata gajiya da surutu ga masifa idan aka yi mata abu ta kama mita wuni za tayi tana abu daya. Inda kuluwa take maryama ta karaso tana cewa kuluwa kinga har mun taso daga makarantar a hanya na hadu da shamsu yace nazo na kiraki, wa zaki Kira? Iyatu ta fada cike da fada to wlh daga yau babu ke babu gidan nan munafuka, dama ashe kece kike hure mata kunne ko? To maza zo ki fice kije ki ce masa ba zata zo ba kuma maza yaje ya nemi matar auran sa amma ba wannan marar asalin ba ehe, kallonta maryama tayi iyatu ni kuma me nayi miki? Daga shigowa ta zaki fada ni da fada kuma naga ai ni ba wani abu na cewa kuluwan ba da zaki ce ina zuga ta, ke maryama ni kike fadawa haka? Saboda tsabar baki da kunya ko, to tun kafin ranki ya baci ki bar min gida idan ba haka ba duk abinda ya biyo baya ke kika jawa kanki, juyawa maryama tayi zan bar miki gida amma ina so ki sani duk abinda mutum ya shuka shi zai girba tana gama fadin haka ta juya tabar gidan, take iyatu ta hayayyako ta fara bala'i tare da jan zaninta tana fadin bari naje na jawa uwar taki kunne kar na kara ganin kafarki a gidan nan tunda abin babu mutunci, nagaji da wannan cin kashin da ake min idan da saninta gwara naji, dagowa da kanta kuluwa tayi tabi bayan iyatu da kallo daidai lokacin da take fita daga soron gidan tasan halin iyatu sarai dama dan ta raba su da maryama da shamsu ne yasa ta takalar fadan, saboda ita dai duk wanda zai kaunaci kuluwa to ita kuma shine abokin gabarta,figar mayafin tayi ta fita tana ta ruwan bala'i ita kam kuluwa ko ba a fada mata ba tasan gidan su maryama ta tafi kai togaciya, haka taci gaba da hada wutar har ta kama ta dora tuwon sayarwar, mahaifinta ne ya fito daga cikin daki ya karaso in da take sannu kuluwa kiyi ta hakuri kinji, komai na duniya yana da iyakar sa shiyasa zaki ji kullum bani da magana sai kiyi hakuri domin shi hakuri baya baci kuma komai yayi farko zai yi karshe ni kaina kin ga hakuri nake da ita amma duk da haka bata barni ba, share kwallar idon ta tayi tace babu komai baba insha Allahu zan ci gaba da hakuri kamar yadda ka bukata, yawwa hawwa'u Allah yayi miki albarka ya baki kyakkyawan rabo duniya da lahira, amin baba tafada tana hawaye, to me ya naji kana sa mata albarka ni kuma sai ka tsine min ai, muryar iyatu suka jiyo daga soro tana magana cikin fushi, in banda munafurci meye zaka wani zo ka saka yarinya a gaba kana zagina a wurinta ko dan ka iya ha'inci sai nayi magana kuma ace ni masifaffiya ce to wlh na fara gajiya ehe, shi dai baban kuluwa sa kai yayi ya fice daga cikin gidan ya bar iyatu tana ta masifa wanda hakan ya zame mata jiki domin kullum wuni za tayi tana babatu a unguwar duk makota suna jinta sai kace ita kadai ce mata, juyowa ga kuluwa tayi tafara yi mata fada duk abinki dai ba zaki auri shamsu ba ke da aure sai dai kiga a nayi amma ba dai ke kiyi ba ita dai kuluwa bata ce komai ba taci gaba da girkin da take yi.

Mangarubar fari ta gama tuwon ta zuba a fanteka ta dauka ta nufi dandali inda a ka'ida can take kaiwa kullum da daddare, tana zuwa tuwon ya kare, kudin da shamsu ya bawa mairo ta bata ta dauka ta siyi abinci taci tayi kat, tana shirin harhada kwanukan ta ne mairo tazo inda take cike da damuwa akan fuskarta, kuluwa kinji abinda iyatu taje ta fada a gidanmu dazu? Girgiza kai kuluwa tayi me tace? Wlh kuluwa iyatu tayi duk wani rashin mutunci da kika sani tare da gargadin shamsu wai babu shi babu ke kuma baki ji zagin da tayiwa iyayen mu ba to shine mahaifin mu yace da shamsu kar ya kara kulaki, wasu hawaye ne suka gangaro akan kumatun kuluwa lallai iyatu ta gama nuna mata kiyayya saboda tunda ta rabata da shamsu ta gama da rayuwar ta,share mata hawayen mairo tayi tace kiyi hakuri kuluwa Allah yasa haka shine mafi alkairi, amin mairo nagode kuluwa ta fada tare da kinkimar kayanta ta nufi gida tana hawaye.

      A haka rayuwar kuluwa taci gaba da guduna cikin ukuba da matsati gashi kaf garin babu saurayin da yake zuwa wurinta saboda kowa tsoron masifar iyatu yake domin dama iya shamsu ne ya jajurce to shima iyatu ta raba su kullum kuluwa cikin kuka take mahaifin ta kuwa hakuri kawai yake bata acikin wannan halin ne aka sanya ranar bikin mairo wadda sai alokacin kuluwa taji hankalinta ya tashi saboda ita da mairo ne kawai suka rage gashi mairon ma zata tafi ta barta nan tabi ta rarrame har mahaifinta ya fahimta ya kirata yayi mata nasiha da cewa tayi hakuri in Allah ya yarda za tayi aure wanda za tayi alfahari da mijin, nasihar mahaifin ta tadauka ta dangana yayinda iyatu ita kuma ta samu nayi kullum habaici wai kuluwa tayi bakin jini bata da saurayi gashi shekarunta 19,kuluwa tun abin yana damunta har ta hakura. Yau da gobe babu wahala har lokacin bikin mairo yazo haka aka sha hidimar biki aka kaita dakin mijinta, bayan bikin da kwana 2 ne kuluwa ta dawo daga talla ta ratsa ta gidan mairo, tsayawa tayi tana kallon dakin mairo wanda yasha kwanukan silba da su dan cana ga gadonta mai runfa na karfe, Allah ya sanya alheri mairo kuluwa tafada kamar za tayi kuka dan tausayin kanta saboda ita tasan babu wanda zai yi mata wannan kayan domin babanta ba shi da hali, zaunar ta mairo tayi ta fara bata labarin irin bakar wuyar da tasha a daren farkonta nan da nan kuluwa tsoro ya shigeta take taji ta fara tsoron maza saboda wannan labarin da mairo ta bata saboda tace mata akwai wuya, yan kayayyakin ta ta dauka ta nufi gida tana tafe tana cewa lallai maza ashe abin tsoro ne, tana zuwa kofar gida ta ga wata dalleliyar mota mai kyau sabuwa dal, gidan ta shiga tana shiga taga iyatu a tsakar gida hankalin ta ashe kamar wadda yan sanda suka kama, jin sallamar ta ya sanya mahaifin ta fitowa daga cikin turakar sa ga wata mata kyakkyawa yar gayu a biye dashi, kallon kulawa matar tayi tace wannan ce hawwan? Lallai hawwa ta girma, amma nayi mamaki ace yarinya kamar wannan bata zuwa makaranta, babu komai Salma ai mun gama magana dake kuje kawai nagode Allah ya bar zumunci, kallon kuluwa yayi yace hawwa ga yar uwata Salma nan da nake baki labari yau tazo zata tafi dake birni zakije kiyi karatu Salma kanwata ce uwa daya uba daya dan Allah ki riketa a matsayin uwa, to abba kuluwa ta fada cikin farin ciki saboda zata bar masifar iyatu, cizon yatsa iyatu ta fara yanzu ina ji ina gani zata tafi da yarinyar nan ta zama irin ta? Inama na barta ta auri shamsun ta kare rayuwar ta a wahala ta fada acikin zuciyar ta, maza shiga ki dauko kayanki inji mahaifin ta, no basai ta dauki komai ba yar gayun ta fada tana murmushi, kama hannun kuluwa tayi tace to zo mu tafi hawwa nan fa iyatu ta biyo su kamar zata kurma ihu tana ji tana gani kuluwa ta shige mota ta dare luntsumemiyar kujera. 
2⃣1⃣
~~~Wani bakin ciki ne ya turnuke iyatu take ta fara masifa tamkar wata zautacciya munafuki dama nasan wata kulalliyar ka kulla saboda yarinyar tana yi min talla tana dan samo min kwabo shine kake bakin ciki, to ai gani nayi dai hawwa yata ce ba taki ba ko? Kuma bake ce kika haifa min ita ba dan haka baki isa kiyi min iko da ita ba yana gama fadin haka ya shige cikin gida nan fa ta bishi tana cewa eh dama ai ka saba yi min gorin haihuwa dan yanzu kayi ba zan ji ciwo ba, shi dai baban kuluwa bai sake tanka mata ba saboda yau burinsa ya cika ya raba kuluwa da wahalar iyatu.

       *************
Gudu anty salma take shararawa a motar ta kamar ba mace ba saboda yadda take tuki babu tsoro a take da ita, sai da suka dan yi nisa sannan ta jiyo ta dubi kuluwa tace hawwa yanzu za kije Inda zaki samu sauyin rayuwa kuma insha Allah zan cikawa yaya burinsa na son yaga kin samu kyakkyawar rayuwa.
2⃣2⃣
Dadi ne ya ratsa zuciyar kuluwa saboda idan da abinda take so to karatu ne ita dai a rayuwar ta tana so ta ganta a makaranta tana daukar darasi, maganar anty salma ce ta katse mata tunanin ta, yaya ya fada min komai game da irin rayuwar da kike yi a hannun iyatu da duk irin tsangwamar da tayi miki, na rasa me yasa iyatu bata da halin kwarai ta dauki duniya ta riketa kamar ba zata barta ba, amma yanzu gashi ai kin tafi kin barta sai muga wanda zata takurawa, shiru kuluwa tayi aranta tace Allah sarki babana yanzu kuma shine zai jure jarabar iyatu tunda ni bana nan.

    Misalin karfe 3 na yamma su kuluwa suka isa garin kanon dabo tumbin giwa wanda masu iya salon magana su kance ko da me kazo an fika, kai tsaye unguwar sharada phase 2 suka wuce, kuluwa zare ido tayi ta fara kalle kallen abubuwan ban mamakin da suke cikin birnin saboda ko motocin dake wucewa abin kallo ne gashi dan adam kamar ba a mutuwa,

suna shiga unguwar kuluwa ta cika da mamaki saboda ganin irin gine ginen dake girke a unguwar kowanne gida ya hadu iya haduwa ga shuke shuke ta ko ina.
2⃣3⃣
Manyan gidaje ne iya ganinka saboda unguwa ce ta masu hannu da shuni, kuma unguwar shiru take babu hayaniya gata tsit kamar babu mutane,

wani babban gida mai bene suka isa anan anty salma tayi hon cikin dan kankanin lokaci wani mai gadi yazo ya bude musu kofar gate din, kutsa kan motar tayi ciki taje tayi packing dinta a inda aka tanada, cikin gidan suka hara wanda yake katoton gaske gashi yasha ginin zamani sai kyalli yake, tana gama kuluwa na biye da ita a baya har cikin wawakeken wani falo wanda ya tsaru iya tsaruwa, kujera anty salma ta nuna mata tace zauna ina zuwa, nan kuluwa ta zauna in banda kalle kalle babu abinda take yi komai na falon bakone a wurin ta shiyasa ta tsaya take ta kallon fallon har anty salma ta fito ta kawo mata abinci ta bata.

Abincin ta fara afkawa har ta koshi sannan ta samu nutsuwa, kallonta anty salma tayi hawwa kin san Ummi? Girgiza kai tayi, Ummi yata ce ita ma ba zaki fita a haife ba, tare zaku zauna a gidan nan saboda dama ni ba anan nake da zama ba, zuwa nake yi lokaci lokaci, yanzu ki taso muje ku gaisa da kishiya ta kafin ummin tazo.
2⃣4⃣
Bin bayan anty salma tayi har zuwa wani hadadden sashe mai mutukar kyau da tsaruwa komai na ciki mai tsada ne,

wata farar mata kyakkyawa ta gani zaune a falo tana ganinsu ta fara fara'a da alama suna zaman lafiya da anty salman, zama kuluwa tayi ta gaida ta ta amsa fuska a sake kamar dama ta santa, maman ummi ga yar tawa wadda zasu zauna da ummi dan Allah idan anga tayi ba daidai ba a tsawatar mata, babu komai anty ai shi da na kowa ne, tashi anty salma tayi tace to zo mu tafi hawwa, binta kuluwa tayi suka fita daga bangaren Maman Ummi suka koma nata suna zuwa suka tarar da har Ummi ta dawo nan kuluwa ta saki baki tana kallon ummi wadda take yar gayu kamar yar India gata dai bata fita a haife ba amma ta iya tsara gayu, zaunar su anty salma tayi ta gabatar wa da kowacce  yar uwarta tare da dorawa ta hanyar cewa hawwa zan samo miki teacher wanda zai rinka yi miki lesson kafin ki fara zuwa makaranta murmushi kuluwa tayi nagode anty salma Allah ya saka da alkairi dama wlh ina son makaranta sosai, kiyi hakuri hawwa zaki yi kinji, to anty na gode. Kwana 2 da zuwan kuluwa ta dan goge tayi fes saboda yanzu bata aikin wahala komai yi musu ake yi sai dai kawai suci su sha su kwanta nan fa kuluwa ta fara hada kiba saboda samun jin dadin da take,

tuni anty salma ta nemo mata lesson teacher wanda zai rinka koyar da ita turanci da sauran subjects din da za tayi a makaranta, ita kuma ummi kullum tana zuwa school safe da yamma a halin yanzu tana ss2 zata shiga ss 3.
2⃣5⃣
  Lokaci ne yaci gaba da tafiya da dafarko kuluwa ta dan fuskanci matsala wajen koyon harshen turanci amma koda ta dage ta maida hankali dandanan ta fara fuskanta kan Ummi A'isha ta ankare tuni kuluwa ta zama baturiya domin ita da ummi yanzu basa hausa komai nasu da turanci suke yi, ganin haka yasa anty salma zuwa tayi mata registration a wata private school mai suna sharada standard boys and girls school, ss 2 suka bata saboda tayi girma ta wuce asata a junior section, sai dai ba makarantar su daya da Ummi ba kowa tasa daban ita ummi inda take zuwa da nisa ita kuma kuluwa babu nisa domin acikin unguwar ne.

Tuni kuluwa ta fara zuwa makaranta uniform dinta riga da skirt ne maroon da hijab fari head tied dinma fari ne tun farkon zuwan ta tasaba da mutane tayi kawaye saboda yadda take da farin jini sai dai kuma wani lokacin ta kan shiga damuwa na rashin babanta a kusa da ita. Yau ma kamar kullum bayan sun gama breakfast dinsu da ummi kuluwa ta tashi zata shiga wanka, kallon ta ummi tayi hawwa yau ba zaki school bane? Zanje mana wanka kawai zanyi saboda bana son naje ina tsami a rainani, um to sai kin fito ni kam na tafi, uniform ummi tasa ta dauki school bag dinta ta tafi ita kuma kuluwa wanka ta shiga ta silla ta fito ta shirya tasha turare tasa wankakken uniform dinta kuma gogagge ta sabi school bag tayi hanyar makaranta tasha safa fara da farin combos  ga school bag dinta baka,

daidai kwanar da zata sada ta da makarantar su ta hango wata bakar mota hadaddiya mai black din glasses kirar KIA Rio, in banda tashin sautin music babu abinda kake ji yana fita daga cikin motar kai kace speakers aka doddora ma motar, motar tana zuwa saitin kuluwa ta shiga cikin wani ruwa wanda ke kwance a tsakiyar hanyar ya hadu da jar kasa yayi jawur, fatsalllll ruwan ya fantsama ajikin kuluwa gaba daya farin hijabinta ya wanke da ruwan kwatar ita kanta fuskar ta sai da ruwan ya jikata, tsayawa kuluwa tayi tana son ganin wanda yayi mata wannan aikin, kamar motar ba zata tsaya ba sai kuma taja ta tsaya a sannu aka bude bangaren mai zaman banza wani dan kyakkyawan sauri ya fito, baiwar Allah kiyi hakuri wlh muna sauri ne ya fada yana kallonta, haba malam wannan wanne irin abune kawai kuna driving without...  Rufe kofar motar yayi ya tako inda take kiyi hakuri dan Allah tsaki kuluwa taja amma gaskiya ba kusan mutuncin dan adam ba domin kun cuceni sai da na gama shirina tsaf har na kusa zuwa school zaku batani da kwata? Hon mai karfi aka matsa daga cikin motar da alama wanda ke cikine ya gaji da jiran na wajen, hakuri yaketa bata amma kuluwa ta rufe idonta taci gaba da yaba masa magana, shi kuma na cikin motar sai hon yake,yayi hon sunfi talatin ganin na wajen yaki zuwa su tafi yasa shi bude kofar motar a fusace ya fito, hmmm ni dai ummi A'isha guy din yayi mugun tafiya da hankali na, dogo ne dan madaidaici fatarsa chocolate colour ce tamkar dan kasar Ethiopia yanada dogon hanci gashi da manyan idanuwa kamar kwai idonsa yake saboda round eyes gare shi, gashin girarsa kamar na mace dan sunada yawa, lebensa jajaye ne sosai ga dan madaidaicin bakinsa, yana da dan saje a fuskarsa,kumatunsa na dama kuma dauke yake da beautiful point, ya tara suma him akansa kamar wanda za a kitsa, kunnensa guda daya yasaka earring fari, haka wuyansa ma yasa sarka fara yar sirirya, yana sanye da bakar riga mai gajeren hannu da shorts trouser iya gwiwar sa,

kamar wani wanda yaga kashi ya fara magana kamar me yin rada, bobo meye haka? Kazo mu tafi kawai kana bata min lokaci, wanda aka kira da suna bobo ne ya kalle shi sorry baka ga abinda muka yi bane? And so what? Me zaka yi mata? Zaka wanke mata ne ko kuwa? Ya fada yana yiwa kuluwa kallon banza,ganin haka yasa kuluwa fashewa da kuka, wlh ban yafe muku ba mamugunta kawai yanzu idan naje makaranta a haka dukana za ayi a wurin assembly sai dai na koma gida, kiyi hakuri yanmata bobo ya fada ba wani hakuri da zanyi wlh ban yafe muku ba,

shi dai classic guy dinnan na jikin motar tsayawa yayi kawai yana kallon ta wannan wacce irin shagwababbiyar yarinya ce? Dan kuka bashi da wuya kawai daga haka sai kuka? Maganar bobo ce ta katse shi JUNIOR ka bata hakuri tunda kaine ka bata ta, wannan ne kuma bata isa ba junior ya fada yana komawa cikin motarsa.
2⃣6⃣
  Kara rushewa da kuka kuluwa tayi tace wlhi sai Allah ya saka min mugaye kawai, sake fitowa daga cikin motar junior yayi yace kai bobo wlhi idan ba ka bar wannan village girl din ba zan iya tafiya na barka ka tsaya sai wasting din time dina kake a banza, tahowa bobo yayi yana cewa double sorry my friend, juyawa kuluwa tayi ta kama hanyar komawa tana tafe tana kuka sai kace wata karamar yarinya, bobo yana shiga motar Junior ya fusge ta aguje kamar zai tashi sama yana driving yana bin wakar omalele, dan kallonsa bobo yayi yarinyar nan ta bani tausayi fa, sai kayi kuma junior yafada lokacin da yake kara gudun motar,kai tsaye unguwar jan bulo kubuga suka shiga dai dai first gate suka karasa wani hamshakin gida ginin dutse da dutse gida ne tangameme kuma katoton gaske very massive, tun daga kofar gidan ga wasu mopol nan da sojoji zaune suna ganin mai shiga da mai fita, kan motar junior ya kutsa cikin gidan,yana shiga yaje yayi packing dinta acikin jerin gwanon yan uwanta, ya fito shima bobo fitowa yayi yana cewa ya bahbah na jira ka ne ko naje kawai? Jeka kawai bobo i will call you letter, ok sai na jika, cikin mai falon gidan junior ya wuce yana tafe yana fito gamida wakar oh my Darling i love you! Da wannan wakar ya karasa cikin falon wanda yake unguwa guda mai karatu duk abinda ka sani na jin dadin rayuwa to an tanade shi acikin wannan falon,

mom dinshi ya hango zaune tana waya da wata fankaceciyar wayar ta tasha ado kamar bata manyanta ba, wani dandatsetsen leshi ruwan kwai tasa a jikin ta takafa dauri kunnenta da wuyanta yasha gold mai girman gaske ga zobuna data zubawa yan yatsunta da takalmi hill a kafarta golden colour, inda take ya karasa yana zuwa ya zauna kusa da ita gamida dora kansa akan cinyar ta, kansa ta fara shafawa kamar wani karamin yaro,muryar ta naji tana cewa hajiya yabi ki siyo min setin gold dan saudia guda daya amma ki hado da komai nasa ajiki ina nufin tun daga kan dan kunnensa, zobensa, awarwaron sa da sarkarsa amma bana son mai araha kuma dan Allah ki zabo na yanmata saboda wata girlfriend din junior ce za tayi birthday shine zai bata a matsayin gift, ok sai kin dawo, daidai lokacin ta kashe wayar ta ajiye ta akusa da ita ta fara lailaya sumar kan junior, junior whats happen? Nothing mom, ok har ka dawo daga wurin exercise din?

Mom na dawo amma zan kara yin wani now now yana gama fadin haka ya tashi ya nufi wani injin motsa jiki wanda ke girke acikin falon, hawa yayi ya fara motsa jikinsa har na tsawon mintuna 20 mom dinshi tana zaune tana kallonsa har ya gama.
2⃣7⃣
   Sai da ya gama ya sauko daga kan gym din kai tsaye dakinsa ya wuce, junior ba kayi breakfast ba fa, zanyi mom kin san ban iya yin break da sassafe sai nan da 11 yanzu bacci nake ji saboda am too tired,to je ka huta maza aje ayi bacci, murmushi yayi ya shige dakinsa wanda yake kayace da kayan alatun more rayuwa, toilet ya fara shiga yayi wanka ya fito yazo ya kunna ac din dakin ya fada kan tafkeken gadonsa wanda ya isa mutum 15 su kwanta ba tare da takura ba domin gadon royal bed ne dan gaske, remote ya dauka ya kamo tashar wakokin turanci a tauraron dan adam ta cikin jibgegiyar plasma tv din dake kafe a bangon dakin nasa, kallo ya fara yi sama sama na wakokin da ake sakawa marassa kyan gani domin wata wakar ma mata ne tsirara suke rawa, yana cikin kallonne bacci ya dauke shi nan ya bararraje ya fara sharar baccinsa.

Ya dan jima yana bacci kafin ya tashi ya shiga toilet yayi brush ya fito, falo ya nufa yana zuwa yaga mom dinsa zaune ita da jawaheer  da gudu jawaheer ta taso tayi hugging dinsa tana sanye da riga da skirt matsattsu, rungume ta yayi tareda bata kiss a kumatu hy jawa yakike? Yaushe kika zo? Naje ai na ganka kana bacci, oh yeah ya fada tareda sakalo hannunta cikin nasa ya nufi wurin mom wadda ke zaune tana kallon su sai faman murmushi take, hannun jawa cikin na junior suka zauna kan kujera,bani labarin boyfriend dinki, ya sunanshi, kafadar sa ta dan doka, kasan ni ai ban fara soyayya ba amma kai bani labarin girlfriend dinka, ni? Ni ban da budurwa amma ina da girlfriends da yawa more than 100, dariya jawa tayi tace ai nasanka da farin jinin yanmata sai alokacin mom tayi magana ai junior kam girlfriends domin akwai ma wadda zata yi birthday next week kinga har gida tazo tayi inviting dinsa, dariya jawa ta fara wa yaga na mamajo, duka junior ya kai mata ta rike hannunsa ni dai ummi A'isha yau mamaki ya gama cika ni, kallon junior mom tayi junior baka yi breakfast bafa, mom ki barshi kawai na yi lunch anjima, what? Baka isa ba junior yanzu zan yi maka dura kamar yadda muka saba, wai mom har yanzu junior bai cin abinci sai kin dura masa? Ai haka yake jawa har yanzu, maza dauko min flask din farfesun nan na dura masa da sauri jawa ta mike zata tashi Junior ya jawota ta fado jikinsa, riketa yayi wlh babu inda zaki je yarinya. 
2⃣8⃣ 
~~~ Mom da kanta taje ta dauko abincin tazo inda yake ta tashi jawa ita kuma ta zauna ai tuni Junior ya bata fuska sai kace wani karamin yaro dan yaye mom ki barni Allah anjima zan ci da yawa, a'a my boy ka daure ka danci ko babu yawa kaji, pls junior yawwa maza bude bakin, naman ta yanko wanda yaji tumatur da albasa da tafarnuwa dakyar junior ya bude dan karamin bakinsa mom ta saka masa naman amma yana hadiyewa yaji zuciyarsa na tashi saboda shi baya son garlic kwata kwata, jin cikinsa yayi ya fara murdawa abunku da shagwababbe tuni ya fara langwabewa mom barshi haka my stomach... Mom karki kara min pls, cikin rudu mom ta kalleshi junior menene? Mom cikina ciwo yake duk yadda aka yi ansa garlic ni kuma bana sonta, a fusace mom ta danna inter come kamar zata tsaga gidan dan kara, aguje ma'aikatan gidan suka shigo cikin tsawa tace ina kukun da yayi girkin nan? Da sauri wani mai green din Kaya yace hajiya bata nan taje gida ta dawo, to yana dawowa ku turo min shi, juyowa tayi ga junior ta rikeshi ta kwantar dashi a jikinta tafara shafa bayansa tana jijjiga shi kamar wani yaron goye, sannu Junior jawa ta fada tare da matsowa kusa dashi, kamo hannun jawa yayi yace zaki iya yin driving ki kai mu country mall? Zan iya mana me zaka yi acan? Zanje ne naci abinci na siyo wasu abubuwan da nake bukata, ok tashi muje, to kije dakina ki dauko key din motar mana suna nan akan bedside drawer dina duk wadda yayi miki ki dauko, tashi jawa tayi ta nufi bedroom dinsa ita kuma mom taci gaba da yi masa sannu tana cewa junior zaka iya zuwa kuwa? Ko dai na aika a siyo maka, mom zan iya zuwa ai cikin nawa ya daina ciwon zanje ne kawai na siyo shawarma da dan fish gasasshe, to junior sai kun dawo, tashi yayi lokacin da jawa ta fito suka fita tare yana rike da hannunta domin shi junior ba wani abu bane ya rike hannun mace ko ya rungume ta harma yayi mata kiss duk wannan is nothing a wurinshi dan har ya saba duk lokacin da ya hadu da friends dinshi mata to hugging da kissing din gaisuwar su, suna fita wayar mom ta fara kara, a hankali ta daga tana cewa hello dadyn junior, yes maman junior ya kuke? Lfy lau, ina junior?
Junior yanzu ya fita zaije country mall shida jawa,
Yaci abinci kuwa?
Wlh dad junior yau baici komai ba,
Haba maman junior why ke ba zaki bashi ba tunda kin san shi ba ci zai yi ba,
Am sorry dad junior wlh na fara bashi sai cikinsa ya kama ciwo ashe abincin akwai garlic aciki shi kuma kasan ba ya sonta,
What? Yanzu yana ina?
Yaji relief har ya fita cin shawarma
Ok wanne kukun ne ya dafa abincin? Ki tabbatar kin sallame shi yabar gidan kafin na dawo,
To shikenan sai ka dawo, katse wayar yayi ya ajiyeta cikin fushi domin a duniya ya tsani abinda zai taba lafiyar junior, zai iya yi masa komai a SANADIN GATAN da yake nuna masa. 
2⃣9⃣
Su junior suna fita county mall suka nufa shi da jawa, ga wani kida da yake tashi tamkar a cinema ko kuma wurin wani kwarya kwaryar party suna tafe suna bin wakar har suka karasa, parking din motar jawa tayi tareda fitowa, hannun junior ta kama suka shiga ciki mutane sai binsu da ido suke duk inda suka wulga idone kawai yake binsu sai dai da yawa daga cikin mutanen wurin kama tun daga ma'aikatan su har masu siyayyar ba suyi mamaki ba kasancewar sun San ko waye junior, kallonsa jawa tayi junior what's all this eyes for? What's the meaning of this all looking?? Gaskiya yan garin nan naku akwai gyara har yanzu baku waye ba you are still villagers wlh, dan murmushi junior yayi, that's why I hate 9ja komai nasu abun kallo ne, yanzu dan na rikeki meye abin kallo?? Tsaki jawa tayi forget about them kawai, zagayawa suka ci gaba dayi har suka tsini abinda suke so suka koma wurin shan ice cream.
     *************
A bangaren kuluwa kuwa tana komawa gida ta kwanta taci gaba da kuka, kullum dama tana kewar mahaifin ta, amma yau sai taji tafi tunashi musamman wannan wulakancin da gayen dazun yayi mata, kuka tayi sosai sannan taji zuciyar ta ta dan nutsu yanzu ta danjita ta dama dama, to amma shi wannan guy din waye shi?? Dan gidan waye?? Hakan halinshi ne ko ita kadai yayiwa?? Dan rainin wayo,tsaki tayi tareda yin juyi, Allah sarki babana yanzu ko wanne hali yake ciki gameda masifar iyatu? Allah sarki kauyen mu, ko ina mairo da shamsu? Kila yanzu shamsu yayi sabuwar budurwa but still i love him,

da wadannan maganganun bacci ya saceta ba ita ta tashi ba har sai da Ummi ta dawo daga makaranta ta sameta tana bacci gashi wurin 2 ko salla bata yi ba, tashinta ummi ta fara, wake up jidda, zumbur ta tashi tana kallon ummi, har kin dawo ummi? Ni yau wani banzan gaye ne yayi min sanadin zuwa sch wlhi, shiyasa duk naji na tsaneshi tun lokacin dana fara ganinshi, zaro ido Ummi tayi hmm jidda ba ason a zurfafa a kiyayya kuma ba ason a zurfafa a soyayya domin duk wanda kaji ka tsana to at the end shi zakaji kana tsananin so, God forbid kuluwa ta fada lokacin da take sauka daga kan gadonsu, to shikenan tunda ba zaki yarda da abinda na fada miki ba, toilet kuluwa ta shige ba tareda tace komai ba

3⃣0⃣
    Zama su junior suka yi shida jawa suna shan ice cream har suka koshi sannan suka tashi suka dauko hanyar dawowa gida amma duk da haka kamar tv haka mutane ke rakasu da ido saboda abun nasu sam babu tsari, shi junior daga shi sai wando iya gwiwa da wata body hug dinshi ga sarka a wuyansa,kunnensa na hagu kuma da dan kunne sannan ga wata suma kaya guda ita kuma jawa tasha wata atamfa super mai tsadar amma kuma dinkin fited gown ne wanda ya matsata tsam sannan ga wani dan ziririn mayafinta data dan yafa a iya kanta amma dashi da babu duk daya, hannun junior ta rike suna tafe suna hira tana dan kai masa duka ko kuma shi ya daki kafadar ta da haka suka karasa inda suka ajiye motarsu suka shiga suka fita suka nufi Gida, lokacin da suka isa gida mom bata cikin falon tana dakinta ta sake wanka da shiri cikin wani kyakkyawan leshi, kai tsaye dakinta junior ya shiga yana zuwa ya zauna ajikinta mom wai sai yaushe dad zai dawo?? Sorry junior ya kusa dawowa nan da gobe zai dawo kaji, gashin kansa ta shafa junior kaci shawarman? Mom naci amma yanzu zanje na dan buga kwallo afilin wasa na, tashi yayi kamar an tsikareshi ya nufi dakinsa jawa tana biye dashi kamar jela, yana shiga ya fara cire kayansa jawa tana tsaye tana jiransa babu ruwanshi da wai jawa tana tsaye tana kallonsa kawai wurin saka wandon ball dinshi ne yaji dan kunya yace jawa close you eyes pls, kaima ka cika problem tafada tareda fita daga dakin, wasu fararen kaya yasa wadanda suke gasu nan lodi lodi sababbi fil, riga da wando da abun hannu da wani dan faffadan hankicif wanda yake daurawa akansa, farin combos yasa da safa fara ya fito a bayan rigar tasa an rubuta junior da manyan baki, number rigar number 1 tun daga nan ummi A'isha ta gane junior dan kwallo ne naji da gani, kansa tsaye ya nufi tsakar gidansu acan ya nufi wani babban fili wanda aka tanadi wurin buga kwallo kala kala kama tun daga, handball, volleyball, football, table tennis, racket ball, basketball da sauransu, wasa ya fara bugawa shi kadai, handball ya fara daga bisani ya fara buga football har bobo abokinsa yazo ya sameshi suka ci gaba da bugawa tare. Washe gari da safe junior yana kwance yana bacci da misalin karfe 11 yaji alamun yar hayaniya agidan, ba dan yaso ba yatashi ya shiga toilet ya fito, kai bari anjima nayi sallar kawai ya fada acikin zuciyarsa tareda fita, dad dinsa ne ya dawo dan haka part din dad din ya nufa yana zuwa ya shiga dakinsa, suna tsaye shida mom tana cire masa babbar rigar sa, welcome dad, yawwa junior, zuwa yayi ya rungume dad din nasa, dad i miss you yafada cikeda shagwaba, kayi hakuri junior, dan murmushi junior yayi dad tunda kadawo ina son zanje abuja yau saboda tun jimawa akwai wata girlfriend dina da na jima ina yimata alqawari cewar zanje nayi mata weekend amma ban samu naje ba, no problem my boy ai sai kaje babu damuwa, dad ya fada cikeda rashin damuwa, dariya mom tayi kuma how many days zakayi junior?? Mom ranar Sunday zan dawo saboda ranar Tuesday zanje kd birthday din teemah, ok to amma junior banda sakaci da cin abinci pls, mom ta fada tana murmushi, dan murmushi junior yayi zan kula mom, juyawa yayi yafita ya koma part din mom yaje ya hau kan gym ya fara motsa jikinsa saboda shi dan ball ne koda yaushe cikin motsa jikinsa yake, sai da ya dan jima sannan yashiga dakinsa yayi wanka yafito ya dauki wata jar t shirt mai gajeren hannu yasa, ya dauki black din trouser ya sa, ya taje sumar kansa ya dauki chain yasa ya makalawa kunnensa earring,wani hadadden agogo samfarin bc yadauka ya daura a hannunsa sannan yaja wani takalmi mai mutukar kyau ja yasa a kafarsa.

3⃣1⃣
Turaren imfact ya fesa ya fito hannunsa rikeda wayoyi manya guda hudu, daya wayar ya kara a kunnensa ya fara magana, hello bobo zo mutafi mana nifa na shirya, ok kana gidan? Ok, fita yayi ya nufi wurin bobo wanda ke zaman jiransa acikin gidan. Karfe 2 suka isa abuja kai tsaye unguwar mai tama suka nufa gidansu Lana girlfriend dinsa wadda ita ba musulma bace kuma iyayenta ma Christian ne sannan itama babanta mai kudine gata da kyau kamar ita tayi kanta, lokacin da su junior suka shiga gidan da gudu Lana tazo ta rungume junior ta fara kissing dinsa, riketa sosai junior yayi yana mai wani dan malalacin murmushi, Lana yakike ya fada yana kanne mata ido daya, hannunsa taja zo muje ciki junior, har cikin falon gidansu ta kaisu anan aka cikasu da cima iri iri harda su burkutu sai dai shi junior baya sha, abincin ma sama sama yaci, hannunsa Lana ta kama zuwa wani shiryayyen daki wanda ya tsaru iya tsaruwa, zauna ka huta junior nasan ka gaji, lumshe idonsa yayi ya zube akan gadon yes of course am tired Lana, zama tayi akusa dashi nasani ai saboda nasan halinka junior, sai dai har yanzu baka sauya ba daga tsautsauran ra'ayinka?? Haba junior kaifa big guy ne you are rich,young, handsome, famous,popularly and adorable guy, ka tsaya ka mori kuruciyar ka, agaskiya am very astonished da naji wai baka making love da kowacce mace, kallonta junior yayi tana sanye da wata yar karamar bakar rigarta iya cinya ko hannu rigar bata dashi, hannunsa yasa ya jawota jikinsa, Lana you are very beautiful and attractive, kamar jira Lana take ta fara shafashi, rigar jikinta ta zame da sauri junior ya rufe idonsa, pls Lana stop it, stop it Lana, don't remove it, Lana ba tareda ta saurareshi ba ta cire rigar ta cillarta can gefe ta makalkale junior,nan ta fara sarrafa shi kasancewar ta ba sabin shiga bace, amma shi junior sabin shigane don duk rashin jinsa da iskancinsa baya neman mata barshi dai da rungumarsu da kiss da rike hannunsu amma baya nemansu sai dai su ne suke nemansa, sai ko yan syrup da yake dan kurbawa saboda tsaro shi dinma ba koda yaushe ba sai dai in yaji ransa ya baci, kafin ya ankara har Lana ta gama tubeshi, tuni tafara nuna masa zulamarta a fili, abunku da sharrin shaidan nan junior yaji ya nemi tunaninsa ya rasa haka ya biyewa Lana suka aikata tabargazar su iya son ransu har na tsawon lukuta masu yawa,

    Kumatunsa Lana ta shafa, junior kace baka iya ba, gashi kuma you make me soo happy, murmushi junior yayi batare da yace mata komai ba, Lana gobe zan koma gida saboda akwai wani wasa da zan buga, cikeda damuwa Lana tace shikenan babu damuwa ni duk lokacin dana bukaceka zan zo, ko parents dinka zasu yi fada?? No, Lana mufa wayayyu ne hakama parent dina basuda matsala, wai dan kin kawo min ziyara ai is nothing, dadi Lana taji saboda dama ta dade tana muradin kasancewar ta da junior.

  Wayewar garin junior yabar abuja shida bobo suka dawo kano, aranar da suka dawo ya taradda dad dinsa ya siyo masa babban doki, nan fa junior ya hau dokin ya fara zaga unguwa, kowanne lungu na unguwar sai da yabi, bobo na biye dashi acikin mota ya kure sauti, haka suka wuni suna abu daya duk sun addabi mutane da tseren doki da mota, ga kidan da yaki karewa.

3⃣2⃣
   Sai da yamma lis tayi sannan junior ya iya hakura ya koma gida yaje ya daure dokinsa daga nan direct dakinsa ya wuce yaje ya fada akan makeken gadonsa, ko takalmin kafarsa bai cire ba haka ya kwanta ya fara bacci. Mom ce ta nufo dakin domin dubashi tana shiga ta ganshi kwance yana bacci inda yake kwance ta karasa ta cire masa takalman dake kafarsa taja blanket ta rufe shi ta juya ta fita tana murmushi domin babu abinda take so irin taga junior cikin farin ciki da nishadi, tana zuwa falo taci karo da kawarta hajiya yabi, barka da zuwa mutanen jidda, mom ta fada tana murmushi, yawwa barkanki dai hajiya Fati, wuri suka samu suka zazzauna, momyn junior ga sakon naki ya iso sarkar da na siyo miki agaskiya mai tsada ce kuma ba ta kananan mutane bace, karbar sarkar mom tayi ta fara duddubata yar siririya amma da gani mai tsada ce, yawwa hajiya yabi dadina dake kin iya zabe, dama junior ne zai bawa wata girlfriend dinshi a matsayin gift saboda zata yi birthday ne next week, mom ta fada cikeda farin ciki, kallonta hajiya yabi ta danyi, ni kuwa hajiya fati sai nake ganin kamar abinda kike yi kuskure ne saboda su yara tasu kyau take bata karko domin duk yadda ka dorasu haka suke tashi, shi junior yanzu bai san rayuwa ba saboda baku koyar dashi ba, abin takaici ne ace wai kina goya masa baya akan yayi abota da wata ya mace wadda baki san ko wacece ba alhalin shi kuma yana baligi, hajiya Fati bafa ya mace bace kadai ke dauko abin magana ba wlh da namiji ma yana daukowa kuma ya kamata ki rinka bincikar abokansa saboda bada kowa zaki barshi yayi abota tunda har yanzu junior yarone karami bana tunanin ya wuce 27, take fuskar mom ta sauya bacin rai karara ya bayyana akan fuskar ta, hajiya yabi dama abinda ya kawoki kenan? Kinzo ne kici min fuska ki zage dana tatas? Daidai lokacin junior ya fito daga daki daga shi sai dan karamin blue din wando da rigarsa yar karama irin na yan ball, tsayawa yayi ba tareda ya kalli ko inda hajiya yabi take ba yace mom wai dan Allah wacce talkative din kika samune haka? Haba wannan matar ta cika surutu tun ina bacci take damuna har sai da ta tasheni, gaskiya ni ban son irin wannan mom, adaina tashina da surutu, cikin kwantar da hankali mom tace yi hakuri yarona, koma ka sake kwanciya kaji, mom ai kun riga da kun tasheni kawai, ni yanzu filin ball zanje.

   Yana gama fadin haka ya juya ya fita yana hararar hajiya yabi saboda duk maganganun data fada acikin kunnensa ne, duk ya jisu, yana fita mom tace hajiya yabi naji maganarki kuma nagode amma dan Allah idan babu damuwa daga yau kar ki kara zuwa gidana, yanzu bari na kawo miki kudin sarkarki, rike baki hajiya yabi tayi hajiya fati daga fadar gaskiya? Allah ya huci zuciyarki,ba tareda mom tace komai ba ta mike ta nufi dakinta mintuna kadan sai gata rikeda kudi rafa rafa sababbi fil, mikawa hajiya yabi tayi, gashi hajiya nagode, tashi hajiya yabi tayi shikenan hajiya fati ubangiji Allah ya sada mu da alkairi, amin mom ta fada lokacin da take barin falon

3⃣3⃣
    Junior yana fita ya dauki bicycle dinsa ja domin dama wani lokacin akan keke yake yawo, filin kwallon unguwarsu bobo ya nufa wato sharada, yana tafe yana jin kidan da ya kure acikin wayarsa ya cuccusa earphone acikin kunnensa, daf da wata kwana ya hango kuluwa, kunu yasha itama tana hangoshi tasha kunu ta bata rai, wucewa yayi ba tareda ya kalletaba, itama bata kalleshi ba ta wuce dama lokacin islamiyya zataje Kuma ita kadai take zuwa domin ummi ita tayi sauka tuntuni, filin kwallon kusa da gidansu bobo junior ya karasa yana zuwa aka fara ihu, saboda ganinsa, sauka yayi daga keken ya shiga filin wasan, take aka fara wasa mai zafi sai daf da magrib sannan suka bar ball din shi kuwa dama junior salla ba wani damunsa tayi ba saboda bai ma cika yinta ba, mota bobo ya dauka yake biye dashi shikuma yana kan keke yana kuma buga kwallo da kafarsa, dai dai kwanar dazu da yaga kuluwa yanzu ma nan ya ganota, da saninsa ya daki ball din da karfi taje ta doki keyar kuluwa da sauri ta juyo, ganin junior ya sata daure fuska, bobo ne ya bude motarsa ya fito, yauma an samu akasi matar junior, da sauri junior ya kalleshi what? God forbid me zanyi da bakar fata, wata harara kuluwa ta aika masa sannan tace ai ko Senior ne bashida wannan matsayin balle wani Junior, God forbid me zanyi da jan lebe? Tsaki junior yaja dalla bobo muje kar kasa wannan village girl din ta bata min rai a banza, gaka nan dan kauye tafada tana murguda baki.

    Kallo junior ya bita dashi, kiyi hakuri matar junior bobo ya fada yana dariya, kallonsa bobo yayi Allah kiyaye na auri yar kauye, ni ma babu abinda zanyi dakai, kudai yi hakuri domin ba asan inda rana zata fadi ba, a yamma saboda acan ta saba faduwa kuluwa ta fada tareda daukar hanyar gida, tana zuwa gida ta fara bawa ummi labari, ummi ina dan rainin hankalin nan na rannan dana fada miki? To yauma mun sake haduwa munyi fada, dariya ummi tayi your fighting partner?? Mijinki zaki cemin ai sai nafi ganewa, sai kiyi kuma, nama fasa baki labarin, kuluwa ta fada tana hararar ummi.

   Shi kam junior kekensa ya murza ya tafi ba tareda ya cewa bobo komai ba yana tafe yana jin wakar p square if do me i do you man......! Bobo kuma yana binsa har suka karasa gidansu junior anan suka rabuda bobo shi ya shiga gida bobo kuma ya juya.

3⃣4⃣
Junior yana shiga cikin gidan ya wuce falon mom Wanda yake tafkeken gaske, kan dining ya hau ya fara kokarin duba abinda zai ci, shinkafa ya diba yar kadan wanda ba zata fi cokali biyar ba ya fara ci ahankali, fuskar kuluwa ya hango lokacin da take musu masifa shida bobo "yi hakuri matar junior" maganar da bobo ya fada ta dawo masa cikin kunnensa," ni me zanyi da jan lebe" amsar da ta bawa bobo itace ta sake dawo masa, murmushi yayi shi kadai lallai wannan yarinyar itama tana ji da kanta, fitowar mom ce ta katse masa tunaninsa, junior whats it? Naga kanata murmushi kai Kadai, babu komai mom amma dai kawai yau babu abinda ke damuna shiyasa naji inata annashuwa, murmushi mom tayi to ga sarkar nan can an kawo maka wadda zaka bawa teemah gift din birthday dinta, tnx mom amma matar nan ta dazu ta bata min rai, meyasa mutane suke da munafurci ne mom? Nifa abinda ake min a garin nan ya fara damuna, wlhi matar nan ta dazu taci darajarki mom da sai na zageta, kayi hakuri junior, mutane sun sako min kai a gaba, na rasa me ka tare musu, tsaki junior ya danyi tareda tashi ya nufi dakinsa yana zuwa ya haye gadonsa ya dauki remote ya kamo tashar music ya fara kalla.

   Koda dare yayi kuluwa bata iya runtsawa ba, tunanin junior kawai take yi, kuma shi take ta hangowa a idonta, zaune ta tashi tabi ummi da kallo wadda ke ta sharar baccinta, junior dinnan fa daga gani ba shiryayye bane kuma ba nagari bane saboda yadda yake sa sarka da dan kunne kai idan ba sani ma kayi ba bazaka taba tsammanin musulmi bane saboda yadda  yake dabi'unsa da halayyar sa, kuma da gani bayaji sannan kuma gagararre ne, to ni yanzu meye nawa na tunaninsa? Ta fada acikin ranta, komawa tayi ta kwanta duk kuwa da cewar ba iya baccin zatayi ba, babu shakka junior ya hadu iya haduwa to amma anya zai so mace kamata wadda ta fito daga kauye?? Tambayar da tayi ta yiwa kanta kenan amma kuma bata da amsa.

  Abangaren junior shima hakan take domin koda ya kwanta domin yin bacci kasawa yayi, tunanin kuluwa ne ya addabi ruhinsa, hakika yasan ya kamu da sonta to amma taya zai furta mata? Shifa yanmata hadaddu ma sune ke cewa suna sonsa ba shine yake cewa yana sonsu ba, ruf da ciki ya juya yayi, yafara shafa keyarsa, tab wannan shine gamo ya fada ahankali, daren ranar da kyar ya samu bacci ya dauke shi,washe gari kuwa sai da yakai 11 akwance yana ta bacci, bayan ya tashi ne yayi wanka ya shirya cikin bakin boxer da jar t shirt mai hoton yan yatsu ajiki, tulin sumarsa ya fara tajewa da cumb bayan ya makala dan karamin dan kunnensa ajikin kunnensa na hagu sannan yasa katuwar sarkarsa wadda tsayinta yazo har kan kirjinsa, cumb din ya dauka ya nufi falo yana tafe yana taje sumarsa yana wakar if u see this baby o.oh she was chop my money, because i don't care, don't care, falon dad dinsa ya nufa yana mai ci gaba da tajar sumarsa, afalo ya tarar dasu dad and mom dinsa suna kan dining suna yin breakfast, good morning dad, mom good morning ya fada lokacin da yake Jan kujerar da zai zauna, morning junior, dad ya fada yana dafa kafadar junior tareda dan murmushi, har an tashi?? Dad na tashi dakyar saboda ina son naje na koyawa dokina tsere, bana son na barshi haka, yana da kyau ai hakan, dad ya fada, junior me zaka ci? Mom ta tambaye shi, mom ki barni yanzu babu abinda zan iya ci saboda koko kawai nake son sha, koko junior?? To ni yanzu ina zan samo maka koko junior?? Mom ki barshi bari naje na dawo, tashi yayi yafita zuwa inda dokinsa yake a daure, kunce shi yayi ya hau ya fito daga cikin gidan, yana fitowa yaci karo da bobo, nan bobo yabi shi a baya sukayi bayan layi, tseren mota da doki suka fara take suka hargitsa unguwar da hayaniya dan suna farawa yara suka taru suka cika da samari suna kallo, wasu yaran ma uniform ne ajikinsu suka ki tafiya makarantar suka tsaya kallo,ganin haka yasa malam ladan wato babban ladanin masallacin unguwar yazo wurin, tunda yaga su junior ne ke yin wasan yaji jikinsa yayi sanyi amma duk da haka dai sai da yayi musu magana, kallon hadarin kaji junior yayi masa kafin yace, malam ladan ai lokacin raba zakkar bai yi ba bare kazo min ko? Haba junior yanzu abinda kake yi a unguwar nan ya kamata? Kai Malam ladan wlhi ba don darajar tsufa ba da sai na zageka, junior ya fada yana masa kallon uku saura kwata, juyawa malam ladan yayi ya nufi gidansu junior domin sanar da mahaifansa, yana tafiya junior ya kalli bobo yace, bobo nifa koko nake sha'awa, wanne irin koko? Koko dai da kasani amma ba wanda ake damawa ba, to wanne irin koko? Kai banza ne wlhi baka ganewa, koko damun Allah, oh to ai yanzu na gane, to ba gobe zamu tafi kd wurin teemah ba ai sai ka sha acan, dan murmushi junior yayi hakane fa kuma kasan teemah big girl ce wlh, amma bari gobe tayi.

3⃣5⃣
  Malam ladan na zuwa gidansu junior ya sanarwa da jami'an tsaron ko shi wanene dan haka basu hanashi shiga ba suka bashi hanya ya wuce, har falon saukar baki aka kaishi, nan ya zauna ya jira har dad ya fito, bayan sun gaisa ne malam ladan ya fara magana kamar haka" Alhaji dama ba wani abune yake tafe dani ba illa wani abu da yake faruwa a unguwar nan game da junior, wani abun yayi? Abba ya tambaya, eh to agaskiya dabi'un junior duk ba masu kyau bane, kullum cika unguwar nan yake da kide kide da wake wake, sannan kuma ga tseren mota da na doki da yanzu yake yi mana acikin unguwar nan saboda ya raina kowa babu wanda zai yi masa magana yaji, dan haka Alhaji a kula da yadda junior yake gudanar da rayuwar sa domin acikin hadisi ingantacce manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace kowannen mu mai kiwo ne kuma za a tambaye shi akan kiwon da aka bashi, shugaba mai kiwone, magidanci mai kiwo ne zai yi bayanin yadda ya gudanar da dukkanin harkar iyalansa da tarbiyar yayansa, wannan ya hadar da yadda ya ciyar dasu ya tufatar dasu, yadda ya sauke nauyin dake kansa nasu, irin tarbiyar da ya basu da kulawar da ya basu, Alhaji sufa "ya"ya amana ce kuma wlhi kowa sai yayiwa Allah bayanin yadda ya tafiyar da tasa amanar wacce Allah ya bashi, yana da kyau iyaye su kula da tarbiyar "yayansu, su kula da irin abokan da yaransu ke abota dasu domin shi aboki yana taka muhimmiyar rawa awurin gurbata rayuwar yara saboda aboki yana da wani tasiri na musamman" tunda malam ladan ya fara bayanansa dad jinsa kawai yake domin shi a duniya ya tsani azo ace masa ga laifin junior,malam ladan nagode da wannan bayanin naka kuma daga yau kar ka kuskura ka kara shigo min gidana, tunda duk kokarin da nake muku bakwa gani, Allah ya baka hakuri Alhaji amma ni aganina gyara kayanka ba ya taba zama sauke mu raba, kuma malam bahaushe yace ka so naka duniya taki shi ka ki shi duniya ta soshi, will you get out from here ko sai na kirawo securities sun fitar dakai? Dad ya fada cikin tsawa, jiki yana rawa malam ladan ya juya ya tafi.

   Cikin Gida dad ya koma yana faman fada haba jama'a wai junior me ya tarewa mutane ne, kowa a unguwar nan idan ya budi baki junior zai ce kowa junior sai kace shi kadai ne d'a to agaskiya nagaji daga yau duk wanda ya kara kawo min maganar junior sai na daureshi, daidai lokacin mom ta fito dadyn junior what's wrong?? Wannan mutumin ne wai wai malam ladan yazo min da wata magana wai junior bashida da'a bashida halayya mai kyau, ni narasa me yasa junior mutane suka sa masa ido, ka kyalesu dadyn junior babu abinda zai faru da danmu duk bakin cikinsu, kama daina kulawa dasu. Ba ajima ba sai ga junior ya shigo, kallonsa dad yayi junior daga yau duk wanda ya kara tarar ka da wata magana ka zazzage shi komai girmansa ni nasaka, dad ai ni ina dawowa ma daga bufday din teemah zan bar kasar zan koma sch saboda nagaji da yan sa idon nan, gara ma ka tafi yafi sauki, mom ta fada tana kallonsu.

   Washe gari da safe su junior suka tafi Kaduna birthday din teemah, awani shahararren hotel Kings palace aka shirya birthday din wanda manyan yarane kawai suka halatta, yanmata gasu nan burjik cikin shiga ta alfarma riga da wando ko riga da skirt wasu kuma doguwar riga, shi kam junior sanye yake cikin wata t shirt black & yellow mai tsada ga wata top da ya dora asama, black din trouser yasa, ga dan kunne ga sarka, yasha face baki sai shan kamshi yake, bobo yana kusa dashi, bayan an zazzauna ne sai ga teemah wadda ta sha kwalliya cikin wata hadaddiyar gown ja mai hannu daya, daga saitin cibiyarta an dan yanke wurin Wanda kana iya hango cibiyar ta, haka ta gaba an tsaga rigar duk cinyarta awaje take, ga kanta babu ko dankwali sai wani gashinta ta yankoshi ta gaba, tana shigowa aka saka tafi tareda sakin kida, kanta tsaye ta wuce kujerar da junior yake zaune ta kamo hannunsa ya taso suka fito tsakiyar fili, tuni aka sakar musu kidan oya shake body.

3⃣6⃣
     Kowa acikin hall din sai da su junior suka burgeshi especially ma shi junior ya tafi da hankalin yanmata da yawa saboda ya hadu iya haduwa, yayi tako ina kyawunsa ya bayyana afili, sai da suka dan chashe sannan aka je wurin yanka cake, hannun teemah junior ya kama suka yanka cake din ya saka mata a baki, yankowa itama tayi ta mika masa, cikeda yanga ya dan bude bakinsa tasa masa, nan aka fara tafi raf raf raf, wani kidan aka saki wanda yanzu kowa da kowa ne ya shigo filin aka fara dancing, tuni filin ya rincabe gashi dama har duhun magrib ya bayyana sai da aka sha rawa iya rawa sannan wutar wurin tayi dif! Numfashi kawai kake ji yana fita sai ko motsin mutane.

  Acikin duhun junior ya kamo kugun teemah zuwa jikinsa, a hankali ya fara magana, baby ina son koko ne fa, cikin wata irin murya yayi maganar, ita teemah bata iya bashi amsa ba saboda jin da tayi yana shafar kirjinta, mannata ajikinsa yayi, ya fara kokarin fitar dasu daga cikin hall din, mutane suka rinka ketarawa suna wucewa har suka fita suka nufi bedroom din da junior yayi masauki acikin hotel din, suna shiga ya dan kalleta, kamar wacce tasha giya sai layi take yi a tsakar dakin, kan gado taje ta fada, takalmin kafarta junior ya cire sannan ya matsa kusa da ita, baby ya za ayi?? Lumshe idonta tayi, kawai kazo kasha kokon ka, ka manta da batun condom ai nasan kai ba kowacce mace ce zata samu kayi making love da ita ba, rungumeta junior yayi tareda zame rigar jikinta, baby bakida abubuwa fa why ba zaki shiga kanti ba? A ghana ana sayar da breast enlargement cream in dai nakoma i will buy it for you, ita dai teemah bata bashi amsa ba saboda ta gama zurfafa, nan fa junior ya fara sarrafa ta babu ji babu gani.

Tsawon lokacin suna abu daya kafin su dawo hayyacinsu, kallon teemah junior yayi ganin tana bacci ya sashi tashi daga shi sai gajeren wando yasa riga ya fice daga dakin, dakin bobo yaje ya fara bugawa, Jim kadan bobo ya bude ya baabah ya akayi ne?? Bobo zai yiyu mu koma kano a yau?? Meya faru? Bobo ya tambaya cikeda mamaki, bobo nifa na fada maka koko nake so kuma wlhi har yanzu ban ji na koshi ba, to ina teemah take yanzu?? Gata can adaki mana, to ka bari gobe da safe sai mu tafi yanzu kaje ka kula da teemah, ok, junior ya fada tare da juyawa ya koma dakin da teemah take.

    Lokacin da gari ya waye sai lokacin teemah ta tashi ta kalli junior yana ta bacci, kiss ta mannawa lebensa tare da sake rungume shi, murmushi ya saki idonsa arufe ya fara shafar na shanunta, teemah zan koma Kn yau saboda sch zan tafi acikin week dinnan kuma akwai wasan da nake son bugawa da zarar na koma ghana, daga kai teemah tayi babu damuwa zanzo sch din naku ai, dagaske?? Dagaske mana,ok ki bari kawai ni zanzo sch dinku weekend kinji, kai ta daga, dakyar suka iya rabuwa teema ta tafi shima ya shirya ya fito domin tafiya kn, akan hanyarsu ya fara bawa bobo labari, bobo har mom fa sai da na fadawa ina sha'awar koko amma mom ba ta gane abinda nake nufi ba, dariya bobo yayi shege baabah da ta dago fa? Da sai tamin aure kwana kusa, amma har yanzu banji ni daidai ba, saboda teemah tana da yan matsaloli ajikinta, bata hada komai ba dan har Lana tafita cikar halitta.

3⃣7⃣
   Murmushi bobo yayi junior ka zama dan bariki fa, rikakke ma kuwa, junior ya fada yana kallonsa, wlhi bobo a matse nake ne to amma ita teemah ba zata iya dani ba, shiyasa na ke son na koma ghana kwana kusa, haka suka ci gaba da hirarsu har suka isa kanon dabo, suna zuwa gidansu junior suka yiwa tsinke, lokacin da suka shiga mom na zaune tasha ado cikin wani leshi blue mai tsada kai da ganinsa kasan naira tayi kuka, ga wata sarkar gold katuwa da tasaka, kusa da ita junior yaje ya zauna tareda kwantar da kansa akan cinyar mom, sannu da zuwa yarona, mom tafada tana shafa kansa a hankali, yawwa mom ina dad? Dad dinka yaje kasar Singapore amma ba jimawa zai yi ba, mom so nake nakoma sch acikin satin nan, junior zaka tafi ka barni, ta fada cikin alhinin rabuwa da danta, mom 1 month kawai zanyi fa nadawo, to yarona Allah ya kaimu, tashi yayi yakarasa cikin dakinsa sai a lokacin tunanin kuluwa ya dawo cikin kwakwalwar sa, zama yayi a gefen gadonsa ya lumshe kyawawan idanuwansa yana tuno kuluwa da shagwabar ta, shi dai yana son yarinya shagwababbiya kuma macen data iya shagwaba tana burge shi sosai, kayansa ya fara hadawa cikin babbar jaka.

    Tun karfe 7 na safe ya shirya driver ya kaishi airport ya tafi kasar ghana. Awanni kadan suka sauka, tunda ya sauka ya hango dayo abokinsa wanda suke karatu tare, gefensa kuma wata hadaddiyar budurwa ce wadda ta tsuke cikin riga da wando, da sauri dayo yazo ya tareshi suka gaisa suka nufi motar da dayo yazo da ita, gidan da suke haya suka tasamma, tun akan hanya junior yake kallon wannan budurwar yana murmushi saboda ta tafi dashi over. Suna zuwa gidansu yayi mata sign da idonshi daya take ta gane abinda yake nufi, murmushi tayi ta fita daga motar shi kuma junior ya fara diban kayanshi ya shigar cikin dakinsa.

  Karfe 6 na yamma Patricia ta shiryo ta nufi dakin junior dama lokacin ya shirya tsaf ita yake jira, Patricia yar asalin kasar Nigeria ce sai dai yaroba ce amma kuma kyakkyawa ce sosai, tana yin knocking ya dan leko ganin itace ya sashi bude kofar a hankali, shiga Patricia tayi tare da fara dan idanuwanta ta lumshe su, tsayawa tayi ta rike kugunta tana kallon junior wanda ya rikice yana kallonta, a hankali taje ta tsaya agabansa, hy! Tafada tana dan jujjuya jikinta, hy! Junior ya daga mata hannu, jikinsa ta matsa sosai takai hannunta kan fuskarsa tana shafa gashin girarsa wanda yake baki wuluk kuma yalwatacce, kana da kyau! Ta fada a hankali, lumshe idonsa junior yayi domin yasha jin wannan Kalmar abakin yan mata da yawa, zip din gaban rigarta ta ja tafara zugewa, nan ta rikita junior suka fara bawa junansu feeling.

Sai da komai ya kammala sannan junior yaji kuluwa ta fado masa arai duk kuwa da cewa bai san sunanta ba kuma sau 2 kacal ya taba ganinta a rayuwarsa to amma duk da haka yana jinta acikin ransa sai dai bai san me yake ji gameda ita ba.

3⃣8⃣
  Kansa ya fara shafawa saboda tunowa da kuluwa da yayi domin ya rasa me yasa tun ranar da ya fara ganinta yaji ta burgeshi kuma shagwabar da tayi ba karamin tsaya masa arai tayi ba. Zare jikinsa yayi daga jikin Patricia domin acewar sa yau yasha koko ya koshi, wayarsa ya dauka ya fita falo ya fara kiran bobo abokinsa, bobo yana dauka yace kaga masoyin koko, dariya junior yayi kamar kuwa kasan yanzu shi na gama sha, kuma yanzu haka fita zanyi, zanje stadium inda zamu buga wasa, good Allah ya baku nasara, amin bobo sai munyi waya, yana katse wayar kiran mom dinshi ya shigo, hello mom, junior ka sauka lfy, lfy lau mom ya gida, junior gida babu dadi saboda baka nan, mom ai bazan jima ba zan dawo, to junior a tsaya dai ayi karatu kaji, tom mom akula min da horse dina pls, karka damu my boy zan kula maka dashi fiyeda yadda zaka kula dashi, thank you so much mom, bye bye, ok bye, da sauri ya tashi ya nufi akwatinsa da yake ajiyar kudi, kudi mai yawa ya dauko ya ajiyewa Patricia a kusa da ita, toilet ya shiga yayi wanka ya fito dama salla ba dadashi da kasa tayi ba dan haka kayansa kawai yasa ya fito ya nufi stadium acikin taxi, yana sauka yashiga rest room dinsu inda anan kowanne dan wasa yake shiryawa, ana ganinsa aka fara murna welcome junior, cikin sauri ya shirya cikin fararen kayansa na ball, riga da wando da safa da combus duk farare da abin hannu, lambar rigarsa lamba 1 ajiki an rubuta JUNIOR da manyan harrufa, filin wasa suka shiga inda zasu buga da Accra Golden stars, su kuma kungiyar su Super Eagles, bayan an fara wasan da kamar minti goma sha biyar junior ya zira kwallaye har guda biyu acikin raga, tuni wuri ya gauraye da hayaniyar magoya baya,junior kam daman wannan abun shine yafi komai burgeshi a harkar kwallo domin yana son yadda mutane suke sonsa sosai, gashi ko ina yaje an ringa nunashi kenan kuma sai abin yazo daidai saboda he's handsome & good looking guy, shi kansa akaran kansa yasan ya hadu shiyasa baya missing target.