spon

Monday, June 25, 2018

Ban Yi Nadamar Kasancewar Adilin Mutum Ba — Buhari

Ban Yi Nadamar Kasancewar Adilin Mutum Ba — Buhari
__¥___
*
Shugaba Muhammad Buhari ya yi ikirarin cewa bai taba yin nadamar kasancewar adilin mutum ba inda ya jaddada cewa yana farin cikin yadda ya hana ‘yan uwansa da makusantarsa daga amfana da wata kwangilar gwamnati.

Shugaban ya yi wannan ikirarin ne a lokacin da al’ummar Urhobo suka ziyarce shi a fadarsa a karkashin jagorancin Sheikh Hadiyyatullahi Abdulrashid inda ya nuna cewa shi bai bada kwangila kuma bai damu ya san wanda aka kwangila ba muddin zai yi aiki mai kyau kuma a farashin da zai karbu ga al’ummar kasa.


#Mikiya

Friday, June 22, 2018

Leonal messi: Yana Kokarin Barin Kasarsa



Leonal messi: Yana Kokarin Barin Kasarsa saboda basayi mai abunda yake so messi yace yana so Yakoma Nigeria a lokacin da yaje kallon wasan Nigeria messi yace bqzai doka wasan agerntina da Nigeria ba domin



Saturday, June 16, 2018

[Video] Olamide Ft. Wizkid – Kana

One of the biggest collaborations of the year so far finally gets the visual treatment. Olamide dishes out the well-anticipated official video to his smash hit single – “Kana” featuring Starboy – Wizkid.
The video was shot in the states and it was directed by Sesan but unfortunately Wizkid is not present in the video.
Watch & Download “Olamide Ft. Wizkid – Kana” below:-

[Music] Olamide, Naira Marley, Falz, Simi, Lil Kesh & Slim Case – Naija Issa Goal

No doubt, Coca Cola has just released one of the biggest song of 2018 titled “Naija Issa Goal“.
What do you expect when you have Olamide, Slim case, Falz, Simi, Lil Kesh, Naira Marleyon just 1 song? Fire right? 🔥🔥
Coke has just raised the bar even more higher as they assembled the finest acts to work on this massive project to support the Super Eagles at the ongoing World Cup Tournament in Russia.
With this, it’s sure Nigeria will bring home the Cup.. Enjoy this hit song and share with your friends. Enjoy!!
Listen & Download “Naija Is A Goal” below:-

Sunday, June 10, 2018

Mixtape: DJ Iriz -Fia Mix

In a bid to make recognition of our hard-working Disc Jockeys (aka DeeJays/DJs) in Nigeria, Core DJs Group present to you (Prince Onifade Idris) Ace DJ Iriz A.K.A Agbomabiwon 2, He’s one of the most respected DeeJay in Ogun State, Nigeria, with his hardworking and he’s a  DeeJay who is adored by many for the depth of his dj skills and mixing dexterity. He’s the second to Agbomabiwon 1 (Ace DJ Hacker Jp).



DJ Iriz surfaces with a new mixtape entitled “FIA”, This features hit singles out there, Keep your playlist updated with this mixtape. 
DOWNLOAD MUSIC HERE

[Music] Rarara -Fulogan Wasu Sunsha Mai Sai Nishi

Sabuwar wakar Dauda Kahuhu Rarara Da Yayiwa Shugaban Kasa Baba Buhari Mai Suna Sai Kayi TAwakar GMB Fulgan Wasu Sunsha Mai Sai NIshi.


Yayin da wasu ke kin shugaba buhari wasu kuma sansa suke da.
DOWNLOAD MUSIC HERE

Saturday, June 9, 2018

[Music] Aminu -Rarara Yaci Kudin Mawaka

Sabuwar wakar da akayiwa rarara wace yaci kudin mawakan APC Naira ” Miliyan Dari ” yadda mawakin yace.
To kawai ku saurari wakar domin kuji mai tazo dashi.

Tuesday, June 5, 2018

Yaran comedy: Buhariyya Episode 2

Yaran comedy Episode 2
wata rana ana zaunane gari yaci wuta ba kudi sai suka gano wata bakalleda sukatafi da gudu ana rigerige suna zuwa aka Fara tureture sai ogansu sai shima yatawo yana zuwa yadauki bakalleda yana budewa kun san mai yagani sai kunkalla zaku sha dariyya

Majalisun Nijeriya Sun Gindaya Wa Shugaba Buhari Wasu Dokoki Guda 12


Majalisun Nijeriya Sun Gindaya Wa Shugaba Buhari Wasu Dokoki Guda 12

...idan bai bi ba za mu dauki mataki, cewar majalisun

Majalisun dokokin Nijeriya sun amince da wasu kudurori 12 da suka ce wajibi ne gwamnatin Muhamadu Buhari ta aiwatar da su ko kuma su dauki mataki.

Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Bukola Saraki ne ya karanta matsayar da suka cima bayan wani zama na musamman da suka yi domin duba halin da kasar take ciki, wanda wasunsu suka ce yana ci gaba da tabarbarewa.

Ya ce majalisun biyu sun amince cewa wajibi ne Shugaba Buhari ya dauki alhakin abubuwan da mutanen da ya nada suke yi, sannan ya dauki mataki kan duk wanda ya saba wa doka da yin barazana ga demokuradiyya.

Suka kara da cewa wajibi ne jami'an tsaro su tunkari kashe-kashen da ake yi a kasar, sannan a daina takura wadanda ake wa kallon 'yan adawa ne ko kuma masu bambancin ra'ayi da bangaren zartarwa.

"Majalisa ba za ta yi wata-wata ba wurin daukar mataki kamar yadda tsarin mulki ya ba ta dama, idan aka ki yin wani abu domin aiwatar da wadannan kudurori da aka a mince da su yau (Talata)".

Wannan zama na zuwa ne a lokacin da rashin jituwa ke kara fitowa fili tsakanin gwamnatin Muhammadu Buhari da kuma shugabannin majalisar.

Kudurori 12

*Kawo karshen kashe-kashe a NajeriyaA daina tsangwama da kuma muzguna wa wadansu 'yan majalisa

*Gwamnati ta rika bin doka da oda

*Shugaban kasa ya dauki mataki kan wadansu wadanda ya nada mukamai

*Ya yi yaki da cin hanci da rashawa tsakaninsa da Allah

*Ya daina sanya baki kan al'amurran da suka shafi majalisar

*Majalisar dokokin kasar za ta fara tuntubar Majalisar Dinkin Duniya don ceto demokradiyyar Nijeriya

*Majalisar za ta tuntubi kungiyoyi masu rajin kare demokradiyya don ceto demokradiyyar kasar

*Shugaban kasa ya magance matsalar rashin aikin yi da kuma talauci a kasar

*Duka majalisoshin biyu sun nuna goyon baya ga shugabancin Bukola Saraki da kuma Yakubu Dogara

*Kuma ba sa goyon shugabancin Sufeto Janar na 'yan sandan Nnjeriya Ibrahim Idris

*Majalisa za ta dauki mataki kamar yadda tsarin mulki ya ba ta dama, idan aka ki yin wani abu.

Wadansu na ganin barazanar daukar matakin da tsarin mulki ya ba su kamar yadda suka yi ikirari zai iya hada wa da yunkurin tsige Shugaba Buhari

A ranar Litinin 'yan sandan kasar suka gayyaci Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Bukola Saraki domin amsa tambayoyi kan zargin daukar nauyin 'yan fashi da makami a mahaifarsa ta jihar Kwara.

Sai dai daga bisani Sanata Saraki ya ce sun shaida masa cewa sun janye gayyatar, kawai suna bukatar "ya amsa ne a rubuce".

Tsoffin 'yan sabuwar PDP sun fasa ganawa da OsinbajoAPC ta sha kaye a hannun PDP a zaben jihar Oyo

Rahotanni sun kuma ce an rage yawan jami'an tsaron farin kaya da ke bin tawagar Saraki da kuma Kakakin Majalisar Wakilai Yakubu Dogara, da kuma mataimakansu.

Wannan batu ne kuma ya sa kungiyar tsoffin 'yan sabuwar PDP, wacce Saraki da Kakakin Majalisar Wakilai Yakubu Dogara ke kan gaba a ciki, suka ce sun dakatar da tattaunawar da suke yi da gwamnatin kasar da kuma jam'iyyar APC.

Suna dai zargin cewa an mayar da su saniyar-ware ne tare da yi musu bi-ta-da-kulli, a gwamnatin da suka taimaka aka kafa.

A baya dai gwamnatin ta sha musanta wannan zargi.

" Dalilin Da Ya Sa Buhari Bai Rattaba Hannu Kan Kasafin Kudin Bana Ba"

" Dalilin Da Ya Sa Buhari Bai Rattaba Hannu Kan Kasafin Kudin Bana Ba"
___¥___
*
Ministan Kasafin kudi da tsare tsaren kasa, Sanata Udoma Udo Udoma ya bayyana cewa a halin yanzu Shugaba Muhammad na nazari kan daftarin kasafin kudin 2018 wanda majalisar tarayya ta mika masa.

Ministan ya ce, yin nazarin ya zama dole don zakulo wuraren da aka tafka Kurakurai da aringizo. Tun watan Nuwamba na shekarar 2017 ne, Buhari ya mikawa majalisar kasafin kudin wanda aka tsara kashe Naira Tiriliyqn 8.6.

Monday, June 4, 2018

RA'AYI: Na San Dai Ba Za A Hana Allah Yi Wa Buhari Hisabi Ba


RA'AYI:  Na San Dai Ba Za A Hana Allah Yi Wa Buhari Hisabi Ba

Daga Zee Taraba

Dan Allah masu yi wa Buhari makauniyar soyayya ida kun isa ku hana Allah ya yi masa hisabi ranar gobe tunda ku ba za ku fada masa gaskiya ba kuma ba za ku bari masu tsoron Allah su fada masa gaskiya ba.

Mun lura abun naku ya soma wuce gona da iri, har ta kai ga kuna zagin Malaman addini akan siyasar banza wadda kwata-kwata duk rantsi duk jimawa shekaru takwas kacal ake akan kujerar.

Mulkin Buhari babu hali Malami ya ce zai fito ya fadawa Buhari gaskiya sai a soma cewa wai malamin siyasa ne, idan kuma ya yaba Buhari sai a ce na addini ne tsabar son zuciya irin namu.

Wai shi Buhari yafi karfi a fada masa gaskiya ne?

A ce wai Malaman addini a ringa zagin su akan wani dan Siyasa wanda kullum shi a yabon kansa yake shi kadai tsabar son rai?

To bara ku ji na fada muku, idan kun hana a fada masa gaskiya a nan gidan duniya, to ku sani baku isa ku hana Allah ya yi masa hissabi ba bisa ga yadda ya gudanar da mulkinsa da kuma rayuwarsa ba ranar gobe.

Saboda haka a yi hattara dan Allah, Siyasa ba hauka bane.

TUNATARWA

TUNATARWA

'Yan Uwa Musulmi Kada A Manta Da Daren Daren 'Lailatu Qadri'

ABUBUWA 15 DA ALLAH YA FIFITA DAREN LAILATUL QADRI AKAN DUKKAN DARARE BAKI DAYA

Daga Aliyu Ahmad

*1-Allah ya zabi wannan dare na lailatul Qadri, ya fifita shi ya daukaka shi cikin falala da daraja da daukaka akan dukkan sauran darare baki daya*

*2-Sanyawa wata sura daga cikin surorin Alqurani mai girma SURATUL QADRI* (Dan girmama sha'anin wannan Dare.

*3-Allah ya girmama sha'anin wannan dare na Lailatul Qadri*

*4-Daren lailatul Qadri dare ne mai albarka mai yawa*

*5-A cikin Daren lailatul Qadri ne Allah ya saukar da Alqurani zuwa saman Duniya a baitul Izza*

*6-Aiyukan ibada a wannan dare ya fi alkairi da matsayi da falala akan dararen watannin dubu wanda babu daren lailatul Qadri*

*7-Wanda ya dace da wannan dare kuma ya yi ibada a cikinsa, ya sami alkairi mai yawa, wanda kuma ya yi asarar wannan dare, to an haramta masa alkairi mai yawa*

*8-Wanda ya raya daren da ibada yana mai imani da kwadayin samun lada,to an gafarta masa abinda ya gabata na zunubansa*

*9-Raya darare goma na karshen Ramadan dan dacewa da Daren Lailatul Qadri, yin hakan sunna ce ta Manzon Allah s.a.w*

*10-Manzon Allah S.A.W ya koyar da yin wannan addu'ar a cikin wannan dare don samun afuwa da gafarar Allah"
*ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺇﻧﻚ ﻋﻔﻮ ﻛﺮﻳﻢ ﺗﺤﺐ ﺍﻟﻌﻔﻮ ﻓﺎﻋﻒ ﻋﻨﻲ*

*11-Mala'iku masu yawa har ma da Shugaban Mala'iku wato Mala'ika Jibrilu suna saukowa cikin wannan dare*

Suna saukowa ne domin yin addu'a da nemawa bayin Allah da suke raya wannan dare da ibada gafara a wajen Allah.

*12-Daren mai aminci da walwala tun daga faduwar rana har zuwa fitowar Alfijir*

*13-A cikin wannan dare ne Allah yake tsarawa da rubuta Arziki da Ajali da sauran al'amurar wannan shekara gaba daya*

*14-Shaidan da rundunarsa ba su iya fitowa dan yada alfasha ga dan Adam a cikin wannan dare*

*15-Nemn Daren Lailatun Qadri da kirdadonsa yana cikin shiriyar Annabi s.a.w*

  Allah ne mafi sani.

*ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺇﻧﻚ ﻋﻔﻮ ﻛﺮﻳﻢ ﺗﺤﺐ ﺍﻟﻌﻔﻮ ﻓﺎﻋﻒ ﻋﻨﻲ

GIYA DA SIGARI ZASUYI TASHIN GORON ZABO A NAJERIYA

GIYA DA SIGARI ZASUYI TASHIN GORON ZABO A NAJERIYA.

A yau akesa ran sabon harajin kudin giya dana taba zai fara aiki a Najeriya,  wata majiya mai tushe  tace ana sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari yasa hannu akan sabon tsarin harajin a yau kuma yafara aiki cikin kwanaki 90 masu zuwa.

A karkashin sabon harajin, Tabar sigari, za'a ma ta karin kashi 20 cikin dari na haraji, yayinda duk karan sigari daya zata samu karin naira 1 a shekarar 2018,  a shekarar 2019 karin haraji zai koma Naira 2 akan duk kara daya, a shekarar 2020 kuma karin harajin zai tashi zuwa Naira 2.90 a duk kara daya.

Shi kuma sabon tsarin harajin giya zai shafi Beer, stout, wines da spirits na shekara 3, daga 2018 zuwa 2020.

Ministan kudi, Misis Kemi Adeosun, tace sabon tsarin harajin giya dana taba sigarin wani matakine  na gwamnati domin rage matsalolin rashin lafiya da ke tattare da taba da giya.

Annobar Amai Da Gudawa Ta Barke A Nasarawa

Annobar Amai Da Gudawa Ta Barke A Nasarawa
___¥__
*
Rahotanni daga jihar Nasarawa sun nuna cewa annobar Amai da Gudawa ta barke a yankin Angwan Lambu da ke karamar hukumar Keffi a jihar Nasarawa.

A halin yanzu dai, annobar ta yi sanadiyyar mutuwar wata mata yayin da wasu mutane 20 suka kamu da annobar wanda ya hada har da wasu daliban jami'ar Nasarawa da ke Keffi. Da yake tabbatar da barkewar annobar, Kakakin Jami'ar, Abraham Ekpo ya ce, ana duba daliban da annobar  ta harba a karamin asibitin jami'ar.

Wasu Mahara Sun Kai Hari Gidan Kurkukun Minna

Wasu Mahara Sun Kai Hari Gidan Kurkukun Minna
___¥___
*
Wasu mahara sun kai wani mummunan hari a gidan kurkukun garin Minna da ke jihar Neja inda suka kashe wani jami'in hukumar kula da gidajen kurkuku tare kuma da arcewa da wasu fursunoni guda biyu.

Kakakin Gidan Kurkukun, Rabi'u Shuaibu ya ce, miyagun sun kai harin ne a daren jiya Lahadi inda suka yi musayar harbe harbe da masu tsaron gidan kurkukun wanda a sakamakon haka suka harbe wani dan Achaba wanda ya kawo wani jami'in gidan kurkukun.

YA KAMATA A DAKATA HAKA NAN


YA KAMATA A DAKATA HAKA NAN

DALILI NA ....

Daga Shehu ladan Army Malumfashi

Watau abin da yasa na bada HAKURI na kuma ce a saurara a kauda kai shi ne, Ina gudun kar rikicin cikin gida ya cinyemu, idan nace cikin gida ina nufin,Musulmai da Arewa da Hausawa da kuri 'unmu.

Sanin kowane abokan zaman mu a Nigeria ba su zabi BUHARI ba a 2015, kuma duk da dumbin ayyukan raya kasa da ya ke tayi masu, karfa ku dauka cewa wai za su zabe shi a 2019.

Mu dai ne muka zabi abin mu da kanmu, kuma mu ne za mu kara zabar shi dai a 2019,To ku daina mugayen kalamai a kan wadanda su ke tare da jama'a, kuma jama'a suke goyon bayansu ko da mabiyansu yan kadanne, domin wadannan kalaman na ku za su iya jawo tsananin kiyayya ga wanda ku ke karewa har tana iya kai ga rasa kuri'ar almajiransu ko mabiyansu.

Misali kun ga akwai gaba da kiyayya da ke ta yaduwa
tsakanin BUHARAWA da ATIKAWA da KWANKWASAWA da TINUBAWA da SHI 'AWA da wasu SANATAWA da wasu WAKILAWA, wannan kowa ya sani, to yanzu kuma za ku cigaba da rura wata sabuwar adawar.

Ku sani duk wadannan kalubale ne a siyasance wanda WALLAHi sun fi karfin a raina su, saboda duk wannan wutar tana ruruwa ne a wuraren da ake sa ran samun
kuri'u masu yawa.

Kuma ku masu kausasa Kalman nan ba ku iya
kawo su, idan aka kwatanta da mabiyan wadanda na ayyana a sama, domin su mabiyan suna jin maganar su, Kar mu dabawa cikinmu wuka.

SHAWARA: Ku zubar da makaman nan haka nan, siyasa ba ta son fada da masu magoya baya da yawa, kuma idan aka maida martani sai a saurara, amma wasu sai cillo makamai masu linzami su ke yi ba kakkautawa,kun ga yanzu wadancan fa dadi za sui ta ji, domin yakin da ya kamata su yi da kansu ne mu ke yi masu, kuma dai kun san zabe yana gab da kurewa ko? Sannan ku kyale shi da yan'uwanshi malamai ku ji ta inda za su bullo ma shi, kamar yadda shi ma BUHARIN ai kun ji yadda yan siyasa su ka yi ma shi dangane da kalaman shi na baya.

To kowace kwarya da abokiyar burminta, Shi
dan siyasa na sosai kullum haduwa ya ke so ba rabuwa ba.

Allah ya kara had'a kawunnan mu Ameen.

[Music] Chizzi D x Kelvin Chuks x OBJ – Shoti Yeh


This one is for the Street 🔥🔥 No Stopping!!
Chizzi D came through with this Shaku Shaku tune titled “Shoti Yeh” and he employed the services of Kelvin Chuks & OBJ to deliver this monster jam off the Oven.
Dope lyrics from the beginning to the end. It’s safe to say, this is one of the best Shaku anthem out there now. Enjoy! 💥
Listen & Download “Chizzi D x Kelvin Chuks x OBJ – Shoti Yeh” below:-

Big Match! Our Super Eagles To Battle Czech Republic On Wednesday @ 2pm (Drop Your Predictions Here)

After going down in a painful defeat to England at Wembley, our Super Eagles will be looking for a confidence-boosting victory when we face Czech Republic.
Unlike Nigeria, the Czechs are not preparing for this summer’s big tournament after they failed to qualify.
Gernot Rohr promised some changes to the side so we can only hope for a better perfomance when we face our opponents on Wednesday.

Sunday, June 3, 2018

Mun kusa hadewa da wasu jam'iyyun adawa don fatattakar APC a 2019 - PDP

Mun kusa hadewa da wasu jam'iyyun adawa don fatattakar APC a 2019 - PDP

Shugaban jam'iyyar adawa ta PDP Prince Uche Secondus ya shaidawa wakilin kamfanin jaridar Punch cewa tuni shirye-shiryen hadewa da sauran jam'iyyun adawa a kasar nan domin kawar da jam'iyyar APC mai mulki a zaben 2019 yayi nisa.

Shugaba Secondus ya bayyana cewa kwamitin da jam'iyyar ta kafa karkashin jagorancin tsohon gwamnan jihar Kuros Ribas na samun gagarumar nasara don kuwa tuni sun kai wani mataki na fahimtar juna da wasu jam'iyyun.

Mun kusa hadewa da wasu jam'iyyun adawa don fatattakar APC a 2019 - PDPKU KARANTA:An mallakawa Yarima Bin Salman ikon Makka da Madina

Sunayen ‘yan ta’addan da ‘yan sanda ke zargin Bukola Saraki da daukan nauyin ayyukan su

Sunayen ‘yan ta’addan da ‘yan sanda ke zargin Bukola Saraki da daukan nauyin ayyukan su

A yau ne hukumar ‘yan sanda ta aike da takardar gayyata ga shugaban majalisar dattijai, Bukola Saraki, bayan wasu gungun ‘yan fashi da aka kama sun bayyana cewar Saraki na daga cikin mutanen da suke yiwa ayyukan ta’addanci.

Hukumar ta ‘yan sanda tace yanzu haka tana tsare da mutane 22 da take zargi da hannu cikin fashin bankunan garin Offa na ranar 5 ga watan Afrilu tare da kashe mutane kimanin mutumin 33.

Ga jerin sunayen mutanen da inda suka fito kamar yadda hukumar ‘yan sanda ta wallafa

Sugabannin gungun 'yan fashin shine:
1. Ayoade Akinnibosun,mai shekaru 37 – daga Oro, Irepodun LGA, Kwara State.

2. Ibukunle Ogunleye, shekaru 36 – daga Oro, Irepodun LGA, Kwara State. Ya kashe mutane 2

3. Adeola Abraham, shekaru 35 – daga Oro, Irepodun LGA, Kwara State. Ya kashe mutane 5

4. Salawudeen Azeez, shekaru 49 – daga Oro, Irepodun LGA, Kwara State. Ya kashe mutane 2

5. Niyi Ogundiran, shekaru 37 –daga Oro, Irepodun LGA, Kwara State.
Ya kashe mutane 2

6. Michael Adikwu,shekaru 30 – Ya kashe mutane 22, yawancin su 'yan sanda.

7. Kabiru Afolabi, shekaru 26

8. Omoseni Kassim, shekaru 28

9. Kayode Opadokun, shekaru 35

10. Kazeem Abdulrasheed, shekaru 36

11. Azeez Abdullahi, shekaru’ 27

12. Adewale Popoola, shekaru 22

13. Adetoyese Muftau, shekaru 23

14. Alexander Reuben, shekaru 39

15. Richard Buba Terry, shekaru 23

16. Peter Jasper Kuunfa, shekaru 23

17. Ikechukwu Ebuka Nnaji shekaru 29

18. Moses Godwin, shekaru 28

19. Adeola omiyale, shekaru 38, daga garin Isanlu Isin, Isin LGA, Kwara State.

20. Femi Idowu, shekaru 34

21. Alabi Olalekan, shekaru 49-mai taimakawa gwamnan jihar Kwara na musamman

22. Yusuf Abdulwahab, shekaru 58 –Shugaban ma'aikatan jihar Kwara.

Kishin-kishin: Shugaba Buhari ya amincewa sifeton 'yan sanda ya kama Saraki

Kishin-kishin: Shugaba Buhari ya amincewa sifeton 'yan sanda ya kama Saraki

A yau, Lahadi, shugaban majalisar dattijai, Bukola Saraki, ya bayyana cewar a shirye yake ya karrama gayyatar da hukumar da ‘yan sanda tayi masa da zarar takardar gayyatar ta same shi.

Kazalika, Saraki ya musanta cewar akwai wata alaka dake tsakanin sa da mutanen da ake zargi da aikata laifin fashin bankunan garin Offa na ranar 5 ga watan Afrilu.

A yau, Lahadi, ne hukumar ‘yan sanda ta bayyana cewar wasu daga cikin wadanda ta kama dangane da batun fashin bankunan garin Offa sun ambaci sunan Saraki da na gwamnan jihar Kwara, Abdulfatah Ahmed, a matsayin mutanen dake daukar nauyin aiyukan su na ta’addanci.

Wata majiya a fadar shugaban kasa ta bayyana cewar shugaba Buhari ya lamuncewa shugaban rundunar ‘yan sandan Najeriya , Ibrahim K. Idris, ya kama Saraki bayan gabatar masa da shaidar samun hannun Saraki a cikin aiyukan ta’addanci, kamar yadda jaridar Premium Times ta rawaito.

Zuwa yanzu Kakakin shugaban kasa da na hukumar ‘yan sanda sun ki cewa komai a kan wannan batu dama kuma batun ganawar shugaba Buhari da shugaban na ‘yan sanda ta ranar juma’a.

Da yake jawabi cikin sanarwar da mai Magana da yawun sa, Yusuph Olaniyonu, ya fitar, Saraki yace alakanta shi da fashi wani makirci ne kawai na bata masa suna.

An kuma: Wasu yan Bindiga sun sake kashe Mutane 23 tare da kona gidagensu a Zamfara

An kuma: Wasu yan Bindiga sun sake kashe Mutane 23 tare da kona gidagensu a Zamfara

A jiya Juma'a ne dai wasu 'yan bindiga suka kashe Mutane har 23 a jihar Zamfara a kauyen Zanoka bayan da suka budewa mazauna kauyen wuta kan mai Uwa da wabi sannan kuma suka cinnawa Gidajen Mutane wuta suka kone kurmus.

Barayin dai sun zo ne kan Babura a matsayin daukar fansar korar da 'yan sintirin yankin su kayi musu inji shugaban karamar hukumar yankin da abin ya faru Mustapha

"Yanzu haka mun binne mutane 23 ciki har da 'yan sintiri da su kayi kokarin dakatar da su."

Mustapha Muhammad ya bayyana cewa 'yan Bindigar sun fara kai farmakin ne ranar Juma'a inda har suka kwacewa Mutane shanunsu sai dai jami'an sintiri na yankin sun fatattake su sannan suka kwato shanun, a dole suka tafi.

Amma sai dai 'yan awanni kadan bayan faruwar hakan sai Barayin suka sake dawowa da babbar runduna kauyen dake nisan Kilomita 160 daga babban birnin Gusau

Kakakin rundunar 'Yan sanda na jihar ta Zamfara Muhammad Shehu ya shaida cewa sun samu gawawwaki 15 bayan da 'yan Bindigar suka kai harin.

"Mafi yawan wadanda suka Mutun 'yan sintiri ne na yankin da su kayi kokarin dakatar da su."

Barayin sun sha kai hare-hare domin sace shanun Mutane tsawon shekaru da dama su kuma kashe duk wani wanda ya nuna tirjiya ga abinda suka aikata.

Wadannan har-hare da ake kai musu ya sanya 'yan Kauyen suka kafa kungiyoyin 'yan sintiri domin tabbatar da tsaro a yankin, amma sai dai su kansu 'yan sintirin ana zarginsu da cin zarafi da kashe wadanda suka kama bisa zargin su.

Yawaitar aiyukan tsagerun ma ya sanya Gwamnati ta kai rundunonin tsaro jihar domin tabbatar da dawo da doka da oda, amma sai dai har yanzu lamarin na dada kamari.

Yaran comedy: Ramadan Kareem Episode 1

Yaran comedy: Ramadan Kareem Episode 1

WA insune suna zaune suna zancen azumi ana zaune sai ga wani mutumi yatawo yana tangadi yana zuwa daidai dasu saiya wadi sai suka tashi sukayo kansa wani yaje yadauko sanda wani yadauko ruwa a buta sai mai sanda yadaga zai bugamasa sai aka rikemasa hannu sukace Kai badan giyabane azumine sai aka yayya famai ruwa ana yayyafa Mai sai yafara nuna bakinsa azuba mai ruwa kasan mai yafaru go an watching TV 📺

Hotunan yadda Aisha Buhari ta yi buda baki da shugabannin Mata

Uwar gidan shugaban Najeriya Aisha Buhari ta yi buda baki tare da shugabannin mata a fadar shugaban kasa.
Aisha Buhari ta yi buda baki tare da shugabannin mata a fadar shugaban kasa a ranar Asabar
Buda bakin ya samu halartar mata daga kungiyoyin fararen hula da ‘yan jarida da kungiyoyin addinai da sauransu.
Daga cikin wadanda aka gayyata buda bakin har da BBC, kuma Raliya Zubairu da Fatima Othman ne suka wakilci BBC
A wajen buda bakin, Uwar gidan shugaban kasa Aisha Buhari da uwar gidan mataimakin shugaban kasa sun gabatar da jawabi

Tsakanin Gwamna Taraba Da Maman Taraba : Ina masu fada saboda yan siyasa? Yanzu mun hankalta?

Tsakanin Gwamna Taraba Da Maman Taraba : Ina masu fada saboda yan siyasa? Yanzu mun hankalta?

Lokacin da maman Taraba Hajiya Jummai Alhassan ke neman kujerar gwamnan Taraba da ita da Gwamna mai ci Darius Ishaku abin ya tashi daga APC da PDP inda abin ya koma na addini.

Daga baya daya kayar da ta sai Buhari ya bata Minista.
Shi yana gwamna ita Minista duka suna samun kudade.

Bayan shekaru kadan sai tace Atiku ne mai gidan ta kuma ko ina zata iya bin shi ta kyale Buhari.

Yau gashi gwamnan Taraba da Maman Taraba suna rike da hannun juna.

Ina magoya bayan nasu daga yan APC da PDP, musulman da kiristocin?
Na tabbata da yawan su na nan babu aikin yi.

GUDUMMAWAR CIBIYAR JIN KAI NA SARKI SALMAN GA NIJERIYA



GUDUMMAWAR CIBIYAR JIN KAI NA SARKI SALMAN GA NIJERIYA

MANUFA
Dukkan musulmi yana sa ne da cewa addinin musulunci ya wajabta taimakon gajiyayyu da raunana da mabukata da wadanda ke cikin ibtila'i, da kiyaye alfarmar ran 'dan adam.

Domin sauke wannan nauyi, mahukunta da 'yan kasar Saudi Arabia suke da dabi'ar taimakawa bil adama a duk fadin duniya, ba tare da la'akari da addini ko jinsi ba. Dabi'ar taimako dabi'a ce da ta shahara da mutanen kasar Saudiyya (musamman a tsakanin mahajjata), sun ciri tuta wurin agaji da jin kai da taimako fiye da duk kasashen Larabawa da Musulmi da ma kasashe masu arzikin man fetur.

Saboda cimma manufar taimako, gwamnatin kasar Saudi Arabia ta kirkiro wannan cibiya maisuna "Cibiyar Bayar Da Tallafin Jin Kai Da Agaji Na Sarki Salman" a turance "King Salman Humanitarian Aid & Relief Centre, KSrelief", ta hanyar tsare-tsare da bayar da kayan agajin jin kai a duk inda ake da bukata a kasashen duniya, domin mutunta Bil' adam da rage asara da radadin talauci. Domin tabbatar da cimma wannan manufa, Sarki Salman Bn Abdul-Aziz ya zuba karin kudi Riyal Biliyan Daya (SR 1,000,000,000) a asusun gudanar da wannan cibiya, kari akan Riyal Biliyan Daya na musamman da ke cikin asusun cibiyar, domin taimakon jin kai ga mutanen Yemen.

An gina gudanar da ayyukan wannan cibiya ne domin cim ma taimakon bil adam.

TARIHI
An kaddamar da wannan cibiya ne a ranar 13/05/2015 a karkashin kulawa da shawarin Khadimul Haramaini Sharifain, Sarki Salman Bn Abdul-Aziz, mutumin da ke ta tarihin sanya hannu kai tsaye a cikin ayyukan jin kai da taimako tun a shekarun baya, musamman a lokacin da yake rike da matsayin Gwamnan Garin Makka. Wannan dabi'a ce ta ci gaba ta haifar da wannan cibiya.

A lokacin kaddamar da wannan cibiya mai babban ofishinta a babban birnin Riyadh, a karkashin gudanarwan babban jami'inta, Dr. Abdullah Bn Abdul-Aziz al-Rabi'a, wanda ya fara aiki da ma'aikata guda hamsin, zuwa yanzu (shekaru uku bayan kaddamarwa) wannan cibiya tana da ma'aikata a fadin duniya kusan mutane dari biyu.

NA GABA-GABA A DUNIYA
Kasar Saudi Arabia tana daga cikin na gaba-gaba a kasashen duniya da suka yi fice wurin bayar da tallafin jin kai da agaji, musamman ga yankuna da kasashen da ibtila'i ya afka musu (kamar: barkewan cuta, girgizan kasa, guguwa, yaki, wutar daji da makamantar su) da kasashen da suke cikin tsananin talauci.

Za a iya sanin haka idan aka yi waiwaye baya, aka yi la'akari da bukatar da Majalisan Dinkin Duniya (UN) ta gabatarwa membobinta daaa kasashen duniya na kudade kimanin Dalar Amurka dari biyu da saba'in da hudu (USD 274 million) domin asusunta na tallafin ayyukan taimako da jin kai. A bugun farko, gudumawar da kasar Saudi Arabia ta bayar na gaba dayan wannan kudi.

AYYUKA DA NASARORI
Daga kaddamar da ita zuwa yau, wannan cibiya ta gabatar da ayyukan taimakon bil adama da bayar da kayan jin kai a kasashen duniya guda talatin da takwas a mabambamtan nahiyoyi (Africa, Asia, Europe and South America). Wannan cibiya tana zartar da ayyukanta ne ta hanyoyi kamar haka:

i. Amfani da tsare-tsaren sa ido akan dukkan kayayyakin taimako da agaji.
ii. Amfani da tsare-tsaren kwararrun masana da abubuwan zirga-zirgan diban kayayyaki tare da hadin kai da mahukunta kasar da za a kai kayayyakin da cibiyoyin Majalisar Dinkin Duniya da kungiyoyi masu zaman kan su a cikin kasashen da za a kai kayan taimakon.

iii. Ana tsara shirye-shiryen (programs) taimako da agaji ne gwargwadon aunawa da tantancewa da dacewan wadanda za a mika musu taimako da tallafi a zababbun wurare da suke da bukata. Kadan daga cikin abubuwan tallafi da taimako da wannan cibiya ke bayarwa sun hada da:
1. Kudade
2. Katifu
3. Barguna
4. Kafa Tantuna
5. Kayayyakin abinci
6. Kayayyakin karatu
7. Gudanar da tantuna
8. Kayayyakin sadarwa
9. Gyara da gina makarantu da ajujuwa
10. Kayayyakin kiwon lafiya da magunguna

Babban dalilin nasara da wannan cibiya ke samu shi ne, hada kai da yin ayyuka tare da cibiyoyin jin kai da taimako na kasa da kasa (international) da na yankuna (regional) da na cikin gida (local) a lokuta da wuraren zartar da ayyukan tallafin jin kai da agaji. Dalilin bin wannan tsari muka samu cim ma kaiwa ga isar da taimako wa miliyoyin mutane a duk fadin duniya.

KASASHEN DA SUKA MORI TALLAFIN KSrelief
1. Afghanistan
2. Albania
3. Algeria
4. Bangladesh
5. Benin
6. Burkina Faso
7. Cameroon
8. Comores
9. Djibouti
10. Eritrea
11. Ethioia
12. Gambia
13. Ghana
14. Honduraa
15. Iraq
16. Jordan
17. Kazakhstan
18. Kyrgyzstan
19. Lebanon
20. Maldives
21. Mauritania
22. Myanmar (Burma)
23. Nicaragua
24. Niger
25. Nigeria
26. Pakistan
27. Palestine
28. Philippines
29. Senegal
30. Somalia
31. Sri Lanka
32. Sudab
33. Syria
34. Tajikistan
35. Tanzania
36. Yemen
37. Zambia
38. Zanzibar

TALLAFIN JIN KAI GA NAJERIYA
Najeriya tana daga cijin jerin kasashen da suka cancanci tallafin jin kai da ayyukan taimako, kasantuwar tana da 'yan gudun hijiran cikin gida (IDP) wadanda rikicin ta'addancin Boko Haram a yankin Arewa Maso Gabashin kasar ya raba su da muhallan su. A ranar 5th/3/2018 tawagar wannan cibiya ta ziyarci garin Maiduguri a yankin Arewa Maso Gabas, inda ta ziyarci sansanonin 'yan gudun hijira ta yi ganin idon ga halin da suke ci. 

A yayin wannan ziyara ne a ranar Litinin, 6th/3/2018 wannan cibiya da hadin gwiwa da Saudi Fund For Development a karkashin jagorancin Nasir Bin Mutlak Alsabi'i (Assistant Dirrector, Emergency Aid Development Of Saudi Arabia) da jami'an wannan cibiya kamar, Khalid Bin Abd Rahman Almani da Muhammad Bin Addida Alnamla, suka kawo kayan gudumawar kayyayakin agaji wa gwamnatin Najeriya na kimanin Naira biliyan uku da miliyan dari shida (N3.6billion), kimanin USD 10million. Gudumawar da ta kunshi kayayyakin da suka hada da: kayan abinci da abinci masu gina jiki da barguna da katifu da tantuna da magunguna da kayan fida (surgical kits) da kudaden ginawa/gyara makarantu da littafai da kayayyakin karatu.

A ranar 8th/3/2018 tawagar ta ziyarci Shugaban Kasar Najeriya, Muhammadu Buhari a Fadar Aso Rock Villa, inda ya yi jawabin godiya ga Khadimul Haramaini Sharifain bisa wannan gagarumin tallafi da jin kai ga 'yan gudun hijira a Najeriya irinsa mafi girma daga wata kasar wwje. Shi kuma jagoran tawagar, Nasir Mutlak ya yi godiyan tarban karimci da gwamnati ta yi musu, tare da ambaton kyakkyawan alakar da ke tsakanin kasashen Saudi Arabia da Najeriya da fatan ganin karshen fitinar ta'addancin Boko Haram.

Don karin bayani a duba: Daily Trust, March 6th, 2018

Marubuci: Muhammad A. Shu'aibu